Saliyo Ta Kaddamar Da Cibiyar Likitancin Gargajiya Na Sin Ta Farko
Published: 2nd, March 2025 GMT
An kaddamar da cibiyar likitancin gargajiya na Sin ta farko, ranar Juma’a a Freetown, babban birnin kasar Saliyo, wadda ta zama muhimmin mataki a yunkurin kasar na amfani da likitancin gargajiya na Sin domin amfanawa al’umma.
Kadammar da cibiyar ta biyo bayan kammala wani aikin binciken kiwon lafiyar al’umma a kasar wanda likitocin kasar Sin suka jagoranta, wanda ke da nufin tallafawa kasar inganta matakan kariya da maganin cututtuka gama gari kamar hawan jinni da ciwo mai tsanin.
Da yake gabatar da jawabi yayin bikin kaddamar da cibiyar, mataimakin ministan lafiya na kasar Saliyo Charles Senessie, ya yabawa dangantaka mai karfi dake tsakanin Sin da Saliyo a bangaren kiwon lafiya, musammam wajen amfani da likitancin gargajiya na Sin. Ya ce Saliyo ta samu nasarori wajen hada likitancin gargajiya na Sin da tsarin kiwon lafiya na kasar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: likitancin gargajiya na Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Gano Babban Yankin Hakar Danyen Mai A Tekun Kudancin Kasar
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp