Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
Published: 2nd, March 2025 GMT
Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa NOA, ta yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na watan Ramadan wajen tunanin abubuwan da za su amfani kasa baki daya.
Kodinetan hukumar na jihar Jigawa Mallam Ahmed Tijjani Ibrahim
ya yi wannan kiran a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.
Malam Ahmed Tijjani ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar zaman lafiya, da tsaro da ci gaban jihar da kasa baki daya.
Ya bayyana watan Ramadan a matsayin wata mai alfarma da ake son musulmi su kara kusanta ga Allah SWT, ta hanyar tsarkake zukatansu.
Don haka Tijjani ya umarce su da su zama ’yan uwan juna, su kasance masu hakuri da kamun kai, da tausaya wa marasa galihu a cikin al’umma.
Ya kara da cewa, NOA za ta bi sahun gwamnatin jihar domin sanya ido da kuma lura da al’amuran da ke gudana a watan Ramadan na wannan shekara domin tabbatar da ganin komi ya tafi yadda ake bukata.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya sake jaddada cewa bikin ya nuna wani muhimmin mataki a ƙoƙarinsa na ƙarfafa wa al’ummar Zamfara masu ƙaramin ƙarfi.
“Saboda haka, cikin farin ciki na tsaya a gabanku domin ƙaddamar da wannan muhimmin shiri.
“Ya ku jama’a, da baƙi, an tsara wannan shiri ne domin bayar da tallafin kuɗi na Naira 75,000.00 kowanne ga masu cin gajiyar shirin su 448,141.
“Kamar yadda Kwamishina Kainuwa ya bayyana a baya, daga cikin adadin da ake sa ran, mutane 279,534 sun cika mafi ƙarancin abin da ake buƙata don karbar Naira 75,000 kowannen su, sauran waɗanda suka ci gajiyar shirin za a tantance su kuma za a ba su nasu da zarar an kammala, In Sha Allahu.
“Ga waɗanda suka ci gajiyar wannan shirin, ina tunatar da kuma gargaɗar ku da kada ku yi amfani da wannan kuɗi wajen biyan buƙatun cikin gida da aka saba yi, wannan ƙarfafawa ce da nufin ba ku damar saka hannun jari a nan gaba don tallafa wa kanku da iyalanku da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikinmu na gida da ma ƙasa baki ɗaya.
“Ina kira gare ku da ku yi amfani da wannan damar ta hanyar da ta dace, ku saka hannun jari a harkokin kasuwanci, kuma ku zama masu dogaro da kai.”
Gwamnan ya gode wa Gwamnatin Tarayya, da abokan hulɗa, da masu ruwa da tsaki, musamman ma ofishin bayar da tallafin kuɗi na ƙasa, bisa jajircewa da bayar da gagarumar gudunmawa ga shirin.
“Bari na yi amfani da wannan dama domin tabbatar muku da cewa gwamnatinmu za ta ci gaba da haɗa kai da kowane mutum ko ƙungiya domin ci gaban jiharmu.
“Da wannan nake farin cikin ƙaddamar da raba katunan cirar kuɗi don sauƙaƙe biyan kuɗin Cash Transfer ga waɗanda suka cancanta.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp