Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
Published: 2nd, March 2025 GMT
Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan, ya bayyana cewa matarsa ta taɓa kawo masa ƙorafi game da cin zarafin da ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya yi mata.
A cewarsa, rikicin ya fara tun lokacin da Natasha ta tsaya takarar kujerar Sanata a 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar SDP, inda ta nemi kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.
A lokacin, Akpabio yana riƙe da mukamin Ministan Neja Delta.
“Da kaina na je na same shi na buƙaci ya bai wa matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotar da ke tsakaninmu.
“Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci,” in ji shi.
Bayan zaɓen 2019, Natasha ta sake tsayawa takarar Sanata a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, inda ta samu nasara.
A lokacin, ana raɗe-raɗin cewa Akpabio bai ji daɗin yadda ta samu goyon baya ba, kuma hakan ya ƙara haddasa rashin jituwa a tsakaninsu.
“Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta ci gaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da ta ke fuskanta daga shugaban majalisar.
“Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fi min ita a yanzu domin ita ce farin cikina.”
Natasha dai ta ce tana da wasu hujojji da za ta fitar, wanda ke nuna yadda Akpabio ya neme ta, lamarin da yanzu haka ya haifar da zazzafar muhawara a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Muhawara Siyasa zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
Shugaban kasar Ukrain Volodomyr Zelesky ya samu tarba mai kyau a kasar Burtaniya bayan ya isa birnin London a jiya Asabar kuma bayan cacan baki mai zafi da yayi da shugaban Amurka Donal Trump a fadar White House dangane da yakin Ukraine.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayyana cewa shugaba Zeleski ya gana da firaiministan kasar Burtania Keir Starmer, wanda ya yaba masa kan yadda ya tsayawa kasarsa da kuma kasashen turai a gaban shugaban Amurka Donal Trump da mataimakinsa a ranar jumma’an da ta gabata.
Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya zanta da shuwagabannin biyu, wato Trump da kuma Zeleski don kwantar da hankali.
A yau Lahadi ce za’a gudanar da taro na musamman kan abinda ya faru tsakanin Zelesky da Trump da kuma makoman kasar Ukraine a yakin da take fafatawa da Rasha tun shekaru 3 da suka gabata.
Sauran shuwagabannin kasashen Turai sun yabawa Zelesky da yadda ya tsayawa kasarsa da kasa kasashen turai a tattaunawarsa mai zafi da manya-manyan Jami’an gwamnatin Amurka.