Jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng ya bayyana a cikin wani jawabi ta bidiyo da ya gabatar ga taron kolin jagorancin Sin na Duke-UNC a ranar 28 ga watan Fabrairu cewa, kasancewar zaman lafiya mai dorewa tsakanin Sin da Amurka a duniya, abu ne da ya zama wajibi kuma nauyi ne dake kan wuyansu.

Xie Feng ya jaddada cewa, idan kasashen biyu suka dauki juna a matsayin abokan hamayya, kuma suka shiga mummunar gasa, kasashen za su yi rashin nasara, kuma duniya za ta sha wahala.

Amma idan suka zama abokan huldar juna, da samun nasara tare, za su samu ci gaba tare, da kuma amfanar da duniya baki daya.

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan An Samu Karuwar Jigilar Kayayyaki A Sabuwar Tashar Jigila Da Ta Hada Sin Da Kasashen Ketare

Ya ce babban abin sawa a gaba shi ne, Amurka ta mutunta ka’idar Sin daya tak, da daidaita batun yankin Taiwan yadda ya kamata, bisa kudurorin dake kunshe cikin takardu uku da Sin da Amurka suka amincewa, da adawa da “‘yancin kan Taiwan”, da daina kyautata alaka tsakanin Amurka da yankin Taiwan, da daina taimakawa yankin Taiwan fadada tasirinsa a wajen kasashen duniya, yin amfani da Taiwan don yaki da Sin zai kawo cikas ga kansa.

Kungiyoyin dalibai na jami’ar Duke da jami’ar North Carolina a Chapel Hill ne suka gudanar da taron kolin jagorancin Sin na Duke-UNC tare.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa

Shugaban Ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce bai ga laifin da ya yi wa Shugaban Amurka Donald Trump, ballantana ya nemi afuwa.

Zelensky ya bayyana haka ne bayan zazzafar cacar-baki da ya kaure a tsakaninsa da Trump a ofishin shugaban ƙasar Amurka.

A cewarsa, “ina godiya ga Amurka da gudunmuwar da take ba mu,” in ji shi kamar yadda ya bayyana a hirarsa da Fox News.

Sai dai ya bayyana cewa musayar yawun ba ta dace ba, sannan ya kara da cewa dangantakar da ke tsakaninsa da Trump za ta gyaru.

Tunda farko dai an soke taron manema labarai da aka shirya yi a fadar White House a jiya Juma’a, inda shugaban Amurka Donald Trump da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky suka shirya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai tsakanin Amurka da Ukraine, bayan wani sa-in-sa mai zafi tsakaninsu biyun a ofishin Trump wato Oval office a safiyar ranar.

Bayan musayar yawun da aka yi a ofishin, Trump ya wallafa wata sanarwa a dandalin sada zumunta na Truth, yana mai cewa, “Na yanke shawarar cewa Shugaba Zelensky bai shirya ma zaman lafiya idan da hannu Amurka a ciki ba. Ya ci mutuncin kasar Amurka a cikin Oval office mai daraja. Zai iya dawowa idan ya shirya ma zaman lafiya.”

A nasa bangaren, Zelensky ya wallafa a dandalin sada zumunta na X cewa, “Zaman lafiya mai dorewa Ukraine ke bukata, kuma muna aiki don samun hakan.”

Haka zalika, shugabar Majalisar Tarayyar Turai Roberta Metsola ta bayyana a dandalin sada zumunta na X cewa, “Za mu ci gaba da yin aiki tare da kai don samun zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu