Leadership News Hausa:
2025-03-03@10:05:13 GMT

Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya

Published: 3rd, March 2025 GMT

Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars wacce ake wa laƙabi da Masu Gida ta doke abokiyar karawarta Enugu Rangers da ci 2-1 a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.

Wasan wanda aka fara da karfe 4 na yammacin ranar Lahadi, ya na daga cikin manyan wasanni masu zafi da ke ɗaukar hankalin masu sha’awar ƙwallon ƙafa a Nijeriya.

Kano Pillars Ta Dakatar Da Kocinta Na Tsawon Makonni Uku Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Rabiu Ali da Jerry Alex ne su ka jefa wa Pillars ƙwallayensu biyu a wasan, da wannan sakamakon Sai Masu Gida su ka koma matsayi na 4 akan teburin gasar Firimiyar Nijeriya.

Ƙungiyar ta Kano ta dakatar da kocinta Usman Abdallah, inda mataimakinsa Ahmed Garba Yaro Yaro ya jagorance ta a wasanni uku na baya bayan nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Enugu Rangers Kano Pillars

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki

Babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada kokarin sa kaimi ga ciyar da shirin kasar Sin mai kwanciyar zuwa matsayi mai girma.

Xi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jagorantar taron nazari na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS a jiya Juma’a. Inda ya yi kira da a ci gaba da kokarin kyautata zaman lafiya a kasar, al’umma su kasance cikin tsari, da kara inganta gudanar da mulkin kasar, kuma jama’a su samu karin gamsuwa. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Natasha-Akpabio: Ƙungiyar Mata Ta Nijeriya Ta Gabatar Da Buƙatu Huɗu
  • Saudiyya Ta Raba Tan Hamsin Na Dabino A Nijeriya
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya
  • Taron Kara Wa Juna Sani Kan Canton Fair Ya Ja Hankalin Masu Masana’antu Da ‘Yan Kasuwan Habasha
  • Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu
  • Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano