Leadership News Hausa:
2025-04-02@15:31:16 GMT

Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya

Published: 3rd, March 2025 GMT

Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars wacce ake wa laƙabi da Masu Gida ta doke abokiyar karawarta Enugu Rangers da ci 2-1 a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.

Wasan wanda aka fara da karfe 4 na yammacin ranar Lahadi, ya na daga cikin manyan wasanni masu zafi da ke ɗaukar hankalin masu sha’awar ƙwallon ƙafa a Nijeriya.

Kano Pillars Ta Dakatar Da Kocinta Na Tsawon Makonni Uku Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Rabiu Ali da Jerry Alex ne su ka jefa wa Pillars ƙwallayensu biyu a wasan, da wannan sakamakon Sai Masu Gida su ka koma matsayi na 4 akan teburin gasar Firimiyar Nijeriya.

Ƙungiyar ta Kano ta dakatar da kocinta Usman Abdallah, inda mataimakinsa Ahmed Garba Yaro Yaro ya jagorance ta a wasanni uku na baya bayan nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Enugu Rangers Kano Pillars

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina

A wani hatsarin mota da ya faru a hanyar Malumfashi-Kafur a Jihar Katsina, mutane tara sun rasu yayin da wasu 11 suka jikkata. Hatsarin dai ya shafi wata babbar motar bas da ke ɗauke da fasinjoji 20. 

Aliyu Ma’aji, Kwamandan Hukumar Kiyaye  Haɗɗura ta ƙasa (FRSC) a jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi. Ya bayyana cewa binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa gaggawar tuki ne ya haifar da hatsarin, inda direban ya rasa ikon sarrafa motar.

An Gabatar Da Motar Asibiti Ta Farko Mai ISO Na Matsayin Kasa Da Kasa A Hukumance Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Kano – FRSC

Haɗarin ya yi sanadin mutuwar mutane tara da ke cikin wata babbar motar bas mai ɗauke da fasinjoji 20, yayin da aka ceci wasu 11 kuma ana jinyar su a asibiti,” in ji Ma’aji. Ya kuma yi kira ga direbobi su guje wa tuƙin gaggawa, jigilar fasinjoji fiye da kima da kuma rashin kulawa yayin lokutan bukukuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Ya Yi Wa Galadiman Kano, Abbas Sanusi, Rasuwa 
  • Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola
  • Kano Pillars Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Kocinta, Usman Abdallah
  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • Kisan ‘Yan Arewa: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kano
  • Gwamnati Za Ta Inganta Wuraren Tarihi Domin Nishadantarwa A Duk Jihohin Nijeriya 
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina