HausaTv:
2025-03-03@16:36:49 GMT

Jagora: Iran Tana Fuskantar  Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai

Published: 3rd, March 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana cewa; al’ummar Iran tana fuskantar makiya kafirai da munafikai, amma kasar ba ta da matsala da sauran al’ummun duniya.

Har ila yau jagoran ya ce, alkur’ani mai girma yana kunshe da hanyoyin da ya kamata a yi mu’amala da dukkanin wadannan makiyan, da kuma lokacin da ya kamata a yi Magana da su, ko kuma lokacin da ya kamata a zare musu takobi.

” Dukkanin wadannan bayanan suna cikin al’kur’ani mai girma.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron karatun alkur’ani mai girma, a jiya Lahadi da dare, ya yi ishara da cutukan ruhi da su ka addabi bil’adama a wannan  zamanin da su ka hada hassada, rowa,mummunan zato, ganda da son kai, da kuma fifita manufa ta kashin kai akan ta al’umma, tare da bayyana cewa, a cikin alkur’ani mai girma da akwai magungunan dukkanin wadannan cutukan.

Jagoran juyin musuluncin ya kuma ce, a bisa mahanga ta musulunci abu na biyu mai muhimmanci bayan tauhidi da ilimi da kyautata alaka da Allah, shi ne shimfida adalci a cikin al’ummar musulmi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu

Rashin kishin wani mutum ya zama abin mamaki bayan ya bayyana cewa, yana zaune lafiya tare da matarsa da suka yi shekara uku da wani saurayinta har ma sun shigo da shi cikin gidansu.

Prince Soy, matashi mai dafa abinci a kasar Japan kuma mai amfani da intanet, wanda ke tallatawa da siyar da abincin gargajiya na kasar na okara granola a intanet, kwanan nan hankali ya koma kansa.

Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja Ramadan: Coci ya ciyar da Musulmi 1,000 a Kaduna

A ranar 8 ga Yuli, ya sanar a shafin sa na sada zumunta na kafar X cewa, matarsa Seira za ta dawo gida bayan ta shafe wata shida tana karatu a kasashen waje kuma za ta dawo tare da sabon saurayinta.

Rubutun da ya wallafa wanda aka yi ta ce-ce-ku-ce a kai ya yi saurin yaɗuwa, inda ya haifar da zazzafar muhawara game da auren Pince Soy da alaƙarta da ɗaya mutumin.

Da alama dai taƙaddamar ba ta damu mijinta na aure ba, wanda a zahiri ya rubuta ziyarar saurayin matarsa ta gajeran bidiyo da samun martani a shafukan sada zumunta da yawa.

“Matata da saurayinta za su zauna tare. Tana karatu a kasar waje kuma tana da sabon saurayi.

“Za ta dawo Japan tare da shi, kuma zai zauna tare da mu, a cewar Prince Soy, wanda ya fada wa mabiyansa a shafin X.

Ya ƙara da cewa ba shi da matsala da tsarin da ba a saba gani ba.

Ya bayyana cewa, Seira ta gaya masa cewa, tana son yin karatu a ƙasar Australia a bara, kuma ya yarda duk da cewa ya yi mamakin shawarar da ta yanke.

Ta tafi a watan Janairu 2024, kuma a watan Mayu, ta furta cewa ta haɗu da wani mutumin Japan wanda daga baya ya zama saurayinta.

Saboda Prince Soy da matarsa a baya sun yanke shawarar kasancewa cikin kyakkyawar dangantaka, ba shi da wata adawa ga sabon saurayinta.

Ya kuma bayyana sakonnin rubutu na abokantaka da ya yi musaya da saurayin matarsa da kuma kyautar Starbucks (ice cream) da ya ba shi don zagayowar ranar haihuwarsa.

“Ban taɓa haduwa da shi ba, don haka ban san abubuwan da yake so ba, kuma na yi tunanin idan na ba shi wani abu mai tsada ba zai samu natsuwa ba, don haka na ba shi wani abu karami mai aminci, kamar tikitin Starbucks,” in ji Prince Soy.

A ranar 12 ga Yuli, Soy ya wallafa bidiyon kansa yana gaisawa da Seira da saurayinta a filin jirgin sama, kuma a cikin makon da ya gabata, ya ci gaba da rubuta tsarin zaman da ba na al’adar aure ba, tare da saurayin, suna tare a gidansu.

Shi da matarsa suna kwanciya a ɗakin kwana, yayin da saurayin nata yana kwana a kan kujera.

Wani lokaci sai matarsa da saurayinta suka sami sabani, sai ya shiga don yin sulhu.

“Na gode masa da gaske lokacin da yake tallafa wa matata yayin da take cikin wahala a kasar waje,” in ji Prince Soy.

“Dole ne ya zama mutum da kowa zai yi sha’awa, ko matata ba za ta faɗa masa ba.”

Ra’ayoyin jama’a a shafukan sada zumunta game da lamarin Prince Soy sun yi ta janwo muhawara, inda wasu suka yaba da niyyarsa ta bijire wa ka’idojin zamantakewa da kuma mutunta yarjejeniyar da aka ƙulla da matarsa game da dangantakarsu da juna, yayin da wasu suka ce ba za su iya fahimtar yadda ya dace da alakar zaman soyayyar mutum uku ba, musamman ganin cewa, bai taba samun wata abokiyar zama ba tun bayan auren Seira.

Dangane da amsar tambayoyi kamar “Me ya sa kake gafarta wa matarka ta yi duk abin da take so?”, sai Prince Soy ya ce, “da farko, kalmar ‘gafara’ ba daidai ba ce.

“Matata ba ta yi laifi ba. Ina son in ga matata tana nuna abin da take so wa kanta, tana yin duk abin da ta ga dama, matar da ba ta nuna abin da take so, ba ta burge ni.”

Prince Soy ya kara da cewa, a koyaushe ya san cewa, sha’awar matarsa ita ce, “samun saurayi,” amma bai taba samun matsala da hakan ba, saboda yana farin ciki matuƙar tana farin ciki.

Ya ce, a wani ɓangare, yana jin tausayin samarin Seira, domin ba za su taɓa samun matsayinsa a cikin zuciyarta ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu
  • Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
  • Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana
  • Kasar Masar Ta Tabbatrawa Falasdinawa, Tana Bayansu Kafin Taron Kasashe Larabawa
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa