HausaTv:
2025-04-02@20:33:02 GMT

Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa

Published: 3rd, March 2025 GMT

Babban jami’in diplomasiyyar kasar Masar ya sanar da cewa; Shirin da kasarsa take da shi na sake gina Gaza, abu ne mai yiyuwa a aikace, kuma za a aiwatar da shi ba tare da an kori mutane su bar Gaza ba.

Badr Abdul’adhy,  ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da fira ministan gwmanatin kwarya-kwaryar Falasdinu gabanin yin taron kasashen larabawa a birnin alkahira.

Ministan harkokin wajen kasar ta Masar ya ce; “Hanya daya tilo ta kawo karshen yawan fadace-fadace, shi ne a  cusa wa Falasdinawa fatan jin cewa,abinda suke mafarki da shi mai yiyuwa ne a aikace,wanda shi ne kafa ‘yantacciyar kasarsu.”

Haka nan kuma ya ce; Shirin da Masar take da shi na sake gina Gaza, mai yiyuwa ne a aikace, kuma cikin wani matsakaicin zango na lokaci, bai kuma bukatar a ce sai mutane sun bar kasarsu.”

 Wannan shirin na Masar dai ya zo ne bayan da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya  ce za a kori Falasdinawa su miliyan biyu daga Gaza saboda sake ginata da kuma yin wasu manyan gine-gine na kasuwanci.

Kalaman na shugaban kasar Amurka sun fuskanci mayar da martani mai tsanani daga Falasdinawa, kasashen Larabawa, da kuma  wasu kasashen turai.

A nashi gefen, Fira ministan Falasdinu Muhammad Mustafa ya bayyana fatansa na samun cikakken goyon bayan kasashen larabawa domin aiwatar da shirin na kasar Masar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mu Leka Shirin “Bunkasa Tagomashin Kirkirarriyar Basira Ta AI” Na Kasar Sin

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • Mu Leka Shirin “Bunkasa Tagomashin Kirkirarriyar Basira Ta AI” Na Kasar Sin
  • Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Arewa Ke Tafiya Kudu Farauta
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon