Aminiya:
2025-04-02@19:34:51 GMT

Saudiyya ta buɗe shafin rajistar masu Itikafi

Published: 3rd, March 2025 GMT

Mahukuntan Saudiyya sun buɗe shafi na musamman domin yin rajista ga masu sha’awar yin ibadar Itikifa a watan Ramadan da muke ciki a ƙasar.

A ranar Lahadi, 1 ga watan Ramadana ne aka sanar da buɗe shafin ga masu sha’awar yin Itikafi ’yan asalin ƙasar da kuma baƙi.

Sanarwar ta bayyana ka’idojin da masu sha’awar za su cika domin samun gudanar da ibadar a kwanaki 10 ma ƙarshen watan Ramadan a masallatan Haramin Makkah da Madina da sauransu masallatan ƙasar.

Bayanan da ake buƙata sun hada da:

Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan

1- Ƙasar mutum: Ta asali ko inda yake zama. Sanarwar ta bayyana cewa wajibi ne mai yin rajistar ya kasance ɗan ƙasar Saudiyya ko ya mallaki takardar iznin zama a can.

2- Wurin yin rajista: Wajibi ne mutum ya kasance a Saudiyya a lokacin da zai yi rajista, domin wanda ke wajen ƙasar ba zai iya shiga shafin ba.

3- Shekaru: Wajibi ne mai yin Itikafi ya shekarunsa su kai aƙalla 18.

4- Yanayin lafiya: An buƙatar ya kasance cikin ƙoshin lafiya ta yadda zai iya gudanar da ibada ba tare da wahala ba. Za a yi wa mutum gwajin duk wasu cututtuka masu tsanani. Idan mutum na buƙatar kulawa ta musamman, wajibi ne ya bayyana a yayin yin rajista.

5- Wa’adin Itikafi: Dole ne mutum ya bai ka’idar kwanakin da ya ɗiba na Itikafi. Lokacin ya fara ne daga ranar 20 ga watan Ramadana zuwa bayan Sallar Isha’ ta ranar jajibirin Ƙaramar Sallah.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadana Saudiyya yin rajista

এছাড়াও পড়ুন:

Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar

Hukumomin Myanmar sun buƙaci ƙasashen duniya su hanzarta tura agaji, yayin da jami’an ceto ke ƙoƙarin gano mutanen da suka maƙale a cikin baraguzan gine-gine.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 sun rasu, 13 sun ɓace a hatsarin jirgin ruwa a Bayelsa
  • Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa
  • Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • BUK Ta Ƙaddamar Da Shafin Intanet Da Ɗalibai Za Su Ke Duba Sakamakon Jarrabawa
  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai