Gwamnatin Yamen Ta Gargadi HKI Da Amurka Kan Cewa Tana Sa Ido A Kan Abinda Ke Faruwa Da Tsagaita Wuta A Gaza
Published: 3rd, March 2025 GMT
Kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta gargadi HKI da kuma Amurka kan cewa, tana sanya ido a kan yadda suke sabawa yarjeniyar budewa juna wuta da suka cimma da su. Musamman yadda HKI ta sabawa yarjeniyar a mashigar Rafah na barin abinci ya shiga Gaza, da kuma bukatar sake tattauna wasu al-amura a yarjeniyar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran nakalto Hazem Al-asad mamba a majalisar siyasa ta kasar Yemen, yana fadar haka, ya kuma kara da cewa, kungiyar a shirye take ta sake shiga yaki da Amurka, a duk lokacinda suka yi kokarin cutar da mutanen Gaza.
Al-Asad ya gargadi gwamnatin Amurka da masu goyon bayan HKI a duk wata cutarwa da zata yiwa mutanen Gaza.
Har’ila yau, wani mamba a majalisar, Nasir-Addeen Amir ya bayyana cewa idanummu na kan abubuwan da suke faruwa a Gaza, sannan hannayenmu suna kan na’urorin bude wuta a kan dukkan abubuwan da suka shafi HKI da Amurka, don kare mutanen Gaza.
Amir ya kara da cewa dukkan makamai masu linzami na kasar Yemen su na cikin shirin komawa yaki idan HKI ko kawayenta suka sake farwa mutanen gaza.
Ya kuma kammala da cewa mayakan ansarullah za su sake budewa jiragen ruwa masu zuwa HKI wuta a tekun maliya da sauran wuraren da ta kaiwa hare-hare a baya bayan an fara yakin Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ICC ta yi kakkausar suka ga Hungary saboda yin watsi da sammacin kama Netanyahu
Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) mai hedkwata a birnin Hague ta yi Allah-wadai da matakin da kasar Hungary ta dauka na kin mutunta sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da zai ziyarci kasar da ke tsakiyar Turai a ranar Alhamis.
Mai magana da yawun kotun, Fadi El Abdallah, ya fada yayin wani taron manema labarai cewa, bai kamata mambobin kotun ICC su yi watsi da hukuncin kotun ba.
Kakakin ya ci gaba da cewa dole ne mambobin kotun su aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke.
Ana sa ran Netanyahu zai isa Budapest a yammacin yau Laraba don ziyarar kwanaki hudu, bisa gayyatar Firaministan Hungary Viktor Orbán.
Shugaban na Hangari mai tsatsauran ra’ayi ya gayyaci takwaransa na Isra’ila duk da tuhumar da ake yi wa Netanyahu a hukumance da laifin amfani da yunwa a matsayin hanyar yaki da kuma aikata laifukan cin zarafin bil’adama a Gaza.
Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC ta bayar da sammacin kama Netanyahu da tsohon ministansa na yaki, Yoav Gallant, bisa zargin laifukan yaki da cin zarafin bil adama a ranar 21 ga Nuwamba, 2024.
An bayar da sammacin ne bayan tantance akwai “kwararen dalilai ” dake cewa Netanyahu da Gallant “da gangan sun hana farar hula a Gaza abuban more rayuwa, ciki har da abinci, ruwa, da magunguna da kuma man fetur da wutar lantarki.” A Gaza.
A matsayinta na mamba a kotun hukunta manyan laifuka ta ICC, dole ne Hungary ta kama Netanyahu da zarar ya isa a tsakiyar nahiyar Turai tare da mika shi ga kotu, saidai duk da haka Hungary, ta fito karara cewa ba za ta mutunta hukunci da bukatun kotun ta ICC ba.