HausaTv:
2025-03-03@18:22:02 GMT

Kwance Damarar Dakarun Hashdu Zai Ragewa Harkokin Tsaron Kasar Iraki Aminci

Published: 3rd, March 2025 GMT

Babban sakataren dakarun Asa’ibu Ahlul Hakki na kasar Iraki ya karyata zancen cewa za’a kwance damarar dakarun Hashdu sha’abi na kasar ta Iraki

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Qais Al-Khaz’ali ya na karyata wannan labarin, ya kuma bayyana haka ne a wani shiri a tashar talabijin ta Al-Irakiyya na kasar ta Iraki a jiya Lahadi.

Al-Khaz’ali ya kara da cewa makaman da suke karkashin kula na Hashdu sha’abi suna karkashin kula mai kyau, don haka babu tsaron cewa za’a yi amfani da su a inda bai dace ba. Ya kuma kara da cewa, tsarin tsaro na kasar ta Iraki yana da matukar muhimmanci garemu. Sannan ya kammala da cewa kwance damarar dakarun Hashdu Ashabi zagon kasa ne ga tsaron kasar ta Iraki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar ta Iraki

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza ta bayyana cewa ba za ta amince da duk wa ta sabon tattaunawa da kuma sauya yarjeniyar tsagaita wuta da aka cimma da HKI dangane da yaki a Gaza ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Mahmoud al-Mardawi wani babban jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa ‘ba zamu tsawaita kashi na farko na yarjeniyar ba, haka ma ba za mu amince da gabatar da sauye –sauye a cikin yarjeniyar ba. Mardawi yace HKI za ta karbi fursinonin da suka rage a hannun Hamas kadai ne, ta hanyar ko tsarin da yarjeniyar ta amince da shi. Ya ce: Benyamin Natanyahu yana, cikin dimwa idan ya na son amfani da yunwa a matsayin makami don samun abinda ya kasa samu da makamai ba. HKI ta bada sanarwan cewa za ta dakatar da dabbaka yarjeniyar sulhu da Hamas bayan an kammala kashi na farko na Yarjeniyar, kuma zai dakatar da shigar abinci yankin Gaza idan an kammala kashi na farko na yarjeniya.

Kafin haka Netanyahu ya ce ya amince da shawarar da jakadan shugaban kasar Amurka Donal Trump, Steve Witkoff ya gabatar na tsawaita bangare na farko a yarjeniyar saboda watan Ramadan.

Kakakin kungiyar Hamas Hazem Wassem ya ce: kungiyar tana tuntubar masu shiga tsakani a aiwatar da yarjeniyar , a kai a kai, don ganin al-amura sun koma kamar yadda yakamata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take
  • Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Junbilat: ‘Yan Sahyoniya Suna Son Tarwatsa Kasar Syria
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Ma’aikatar Tsaron Jama’ar Sin Na Matukar Adawa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Karin Haraji
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Kwararrun Masana Sun Gargadi Kan Karkatar da Kudaden Fansho Na Biliyan ₦ 758
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a