HausaTv:
2025-05-07@00:59:57 GMT

Kwance Damarar Dakarun Hashdu Zai Ragewa Harkokin Tsaron Kasar Iraki Aminci

Published: 3rd, March 2025 GMT

Babban sakataren dakarun Asa’ibu Ahlul Hakki na kasar Iraki ya karyata zancen cewa za’a kwance damarar dakarun Hashdu sha’abi na kasar ta Iraki

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Qais Al-Khaz’ali ya na karyata wannan labarin, ya kuma bayyana haka ne a wani shiri a tashar talabijin ta Al-Irakiyya na kasar ta Iraki a jiya Lahadi.

Al-Khaz’ali ya kara da cewa makaman da suke karkashin kula na Hashdu sha’abi suna karkashin kula mai kyau, don haka babu tsaron cewa za’a yi amfani da su a inda bai dace ba. Ya kuma kara da cewa, tsarin tsaro na kasar ta Iraki yana da matukar muhimmanci garemu. Sannan ya kammala da cewa kwance damarar dakarun Hashdu Ashabi zagon kasa ne ga tsaron kasar ta Iraki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar ta Iraki

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa: Gaza na gaf da afkawa cikin babbar masifa saboda zaluncin ‘yan mamayar Isra’ila

A yayin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke ci gaba da killace Zirin Gaza sama da watanni biyu, abubuwan da ke faruwa a kowace rana, abubuwa ne da suke yadda bala’i ke shafar kowane gida, kowane titi, da kowane yaro, tare da cewa a kowace rana, ana kara gargadin cewa; Lokaci ya fara kurewa don ceton abin da za a iya cetowa.

Ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sabunta gargadi game da bala’in da ke tafe saboda ci gaba da rufe mashigar yankin da kuma tsaurara matakan hana shigowa da madarar jarirai, da abinci mai gina jiki, da kuma taimakon jin kai.

Hakan ya wurga yara sama da 70,000 cikin fuskantar matsalar Rashin abinci mai gina jiki, yayin da wasu yaran Falasdinawa ‘yan kasa da shekaru biyar 3,500 ke fuskantar barazanar yunwa. Kimanin yara 290,000 ne ke gab da mutuwa, yayin da fiye da yara miliyan daya ke fama da rashin isasshen abinci a kullum rana. Ofishin ya bayyana wannan lamari a matsayin kisan kiyashi da aka yi a cikin abin kunya da kasashen duniya suka yi shiru, inda ya yi kira da a dauki matakin gaggawa don kawar da wannan killacewar tare da kin ba da damar shigar da kayan agajin jin kai domin ceto rayukan yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bukhaiti: HKI Ta Ketari Jan Layimmu, Ta Jira Maida Martanimmu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
  • Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar
  • OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
  • Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 
  • Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum
  • Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Fararen Hula Kusan 300 A Hare-Haren Baya-Bayan Nan A Sudan