Aminiya:
2025-03-03@21:11:52 GMT

Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yara

Published: 3rd, March 2025 GMT

A wani yunkuri na kawo karshen bautar da kananan yara a Najeriya, Kungiyar Kwadago ta Duniya (ILO ) ta horas da masu ruwa da tsaki kan tsaron sana’o’i da kuma yakar bautar da yara a aikin hakar ma’adanai.

Kungiyar da ke kula da wurare hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ta shirya taron ne da nufin ķarfafa guiwar masu ruwa da tsaki domin kawo karshen bautar da yara a wuraren hakar ma’adinai a jihohin Neja da Osun.

Taron da ya gudanan daga ranar 18 zuwa 27 na watan Fabarirun 2025, wakilan gwamnati da kungiyoyin ma’aikata da shuwagabannin yankunan sun hallara, inda suka tattaun kan hanyoyin kawo karshen matsalar.

Kazalika an bai wa mambobin kwamitin sanya ido kan ayyukan bautar da yara na jihohin kayan aiki da za su taimaka musu wajen sanya ido kuma da kai rahoton game da bautar a kananan yara.

Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu Ramadan: Coci ya ciyar da Musulmi 1,000 a Kaduna

A jawabinta, Daraktan kungiyar kwadago ta Najeriya, Dakta Vanessa Phala, wacce ta samu wakilcin mai kula da ayyuka na kungiyar ACCEL Africa, Misis Celine Oni, ta jaddada cewa za a aiwatar da dokoki da tsare-tsare da za su taimaka wajen kawo karshen wannan matsala.

Kudurin karfo na shirin ACCEL Africa shi ne, aiki tare da ma’aikatun kwadago da na bunkasa ayyuka da na noma, da na ma’adanai da dai sauransu.

Na biyu shi ne, daukar mataki kan sabubban bautar da yara a wuraren haķar ma’adanai, da kuma mai da hankali kan samar da kariya da kudade da kiwon lafiya da kuma aikin yi ga matasa.

Ta jaddada cewa za a magance matsalar bautar da yara, wadda ta ce talauci da rashin samun kariya ne kan gaba wajen haifar da su.

Kwanturola na ma’aikatar kwadago da inganta aiki ta kasa ta Jihar Neja, Hauwa Zakariyya, ta ce, “samar da tsaro da kiwon lafiya hakki ne a kan kowa, kuma ba za a samu wata ci gaba ba tare da tsaro ba.

“Shi ya sa muke daukar wannan kungiya ta ACCEL Africa da muhimmanci, saboda ta mayar da hankali kan wuraren haķar ma’adanai, domin daile aukuwar irin irin abin da ya faru a yankin Kuchiko, inda aka rasa rayuka da dama ciki har da yara kanana. Mun yi imanin cewar wannan tsari zai ilimantar da masu hakar ma’adanai yadda za su kare kansu a nan gaba.”

A nasa bangaren, kwantorulan na ma’aikatar kwadago na Jihar Osun, Solomon Ayinde Alabi, ya ce, “Muna murna da samun rahoto da ke tabbatar da cewa ficewar yara daga makarantu ya ragu sosai. Wannan babban labari ne gare mu a irin wadannan yankuna”.

“Ina kira gare mu a matsayinmu na iyaye  masu kulawa, da al’umma da mu yi amfani da wannan dama da kyau wajen kara azama wajen yaki da ta’addanci, bautar da yara a yankunanmu.”

Mahalarta taron sun ziyarci wuraren haķar ma’adanai a jihohi mabambata don gano hadarin da ke tattare da wannan aiki. Wani dan shekaraa Lawali Yusuf daga cikin masu haķar ma’adanai a Korokwa da ke Minna na jihar Neja ya ce, “ina wannan aiki ne saboda iyayena ba su da karfin daukar nauyin karatuna, shi ya sa nake yi don na tara kudi na fara zuwa makaranta kamar sauran abokaina.”

A yankin Idoka da ke Osun, wani dan shekara 11, Ibrahim da ke hakar ma’adanai ya ce, “burina shi ne zama mai hakar ma’adanai idan na girma, don haka ne ma na zo nan a matsayin yaron gida. Ina so na koyi yadda ake hako zinari duk da ma dai sau da dama ana kora ta daga wurin, sai dai ina dawowa saboda muradina ke nan zama mai haķar ma’adanai.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bauatar da kananan yara hakar ma adainai yara bautar da yara a haķar ma adanai hakar ma adanai kawo karshen

এছাড়াও পড়ুন:

Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria

Malamai daga makarantun firamare 116 dake karamar hukumar Zaria sun gudanar da taron addu’o’i na musamman ga shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen da gwamnatin jihar Kaduna.

Malaman sun gudanar da addu’o’in ne domin nuna farinciki da godiya bisa yadda suke matukar kula da ilimi,wanda hakan ya inganta harkokin ilimin kuma ya kara bunkasa jin dadin Malaman yankin.

Sakatariyar ilimi ta karamar hukumar Zaria, Dr Hassana Lawal ta shedawa manema labaru lokacin addu’o’in a zaria cewa a kalla Malaman makarantun firamare 2,225 ne suka amfana da tallafin kayan abinci domin gudanar da azumin watan Ramadan.

A cewar ta,kayan abincin sun hada da kilo 25 na shinkafa da lita 4 na man gyada da fakitin tafiya da kuma kilo 10 na buhun garin samabita.

“Wannan shine karo na 8 da shugaban majalisar wakilan ya baiwa malaman makarantar firamaren irin wannan tallafin tun daga lokacin da hau karagar shugabancin majalisar.

“Baya ga tallafin kayan abinci,ya baiwa duk shugabannin makarantun firamare 116 da ke yankin kyautar babura domin saukaka masu zuwa wurin aiki,wanda a cewar ta abin godiya ne matuka”.

Haka kuma sakatariyar ilimin ta yaba da kokarin da gwamnan jihar kaduna, Malam Uba Sani ke yi na bunkasa ilimi a jihar.

Dr Lawal ta ce kokarin da gwamnan ke yi sun kushi gina ajujuwa 12 a makarantun firamare da dama a karamar hukumar Zaria baya ga tallafin kayan karatu, wanda hakan ne yasa dole su yi masu addu’o’in.

Ta kara da cewa Malaman sun zami watan Ramadan ne domin gudanar da addu’o’in Allah ya baiwa shugaban majalisar wakilai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi nasara da kwarin gwiwa wajen ci gaba da bunkasa ilimi a jihar.

A nashi jawabin, sakataren Kungiyar malamai na karamar hukumar Zaria, Malam Kasimu Mohammed ya ce tallafin kayan abincin ya taimaka wa Malaman matukar gaske.

A don haka sai ya bukaci sauran yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi shugaban majalisar wakilan ta hanyar tallafawa Malaman makarantun firamare a yankunan su.

Haliru Hamza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji A Gaza
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato
  • Masana’antar Kannywood: Da Tsohuwar Zuma… -Fassarar Farfesa Uba Adamu
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya
  • Taron Kara Wa Juna Sani Kan Canton Fair Ya Ja Hankalin Masu Masana’antu Da ‘Yan Kasuwan Habasha