Karamar hukumar Malam Madori da ke jihar Jigawa, ta yi barazanar daukar matakin hukunta malaman makaranta da ba sa  zuwa aiki.

Shugaban karamar hukumar, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas ya bayyana haka a wata hira da manema labarai bayan raba kudi dubu hamsin a matsayin tallafin karatu ga dalibai ashirin da biyar a yankin.

A cewarsa, wani bincike da aka gudanar  bayan hawansa karagar mulki, ya nuna cewa malaman makarantu da dama ba kasafai suke zuwa aiki ba.

Ya ce hakan na daga cikin dalilan tabarbarewar ilimi a yankin, wanda ke bukatar kulawar gaggawa.

Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas ya yi nuni da cewa, “Ilimi muhimmin abu ne a kowane fanni na rayuwar dan Adam, don haka ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wani malamin da ba ya zuwa makaranta”.

Ya yi nuni da cewa, akwai mutane da dama wadanda suka kammala karatu kuna ba su sami aiki ba, saboda haka za a iya daukarsu fomin maye gurbin wadanda ba sa son zuwa aiki.

Shugaban ya kuma shawarci matasan yankin da su sadaukar da kansu wajen samun ilimi mai inganci, domin cigaban rayuwarsu da kasa baki daya.

Ya kara da cewa, karamar hukumar karkashin jagorancinsa za ta ci gaba da bayar da tallafi ga ilimi, domin samar da ’ya’ya masu ilimi a nan gaba.

.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa

Gwamnatin Amurka ta kakabawa kamfanonin kasar Iran sabbin takunkumi, duk da tattaunawar da ake yi kan shirin nukiliyar.  

Ofishin kula da kadarorin waje na ma’aikatar baitul malin Amurka (OFAC) ya sanar a cikin wata sanarwa jiya Talata cewa, ya kara sunan wani dan kasuwa dan kasar Iran, Seyyed Assadollah Emamjomeh da kamfaninsa cikin jerin takunkumin da aka kakabawa Iran bisa zarginsu da hannu wajen fitar da danyen mai da iskar gas a Iran.

Amurka ta yi zargin cewa Emamjomeh da mukarrabansa ne ke da alhakin jigilar danyen mai na iran da aka kiyasta ya kai daruruwan miliyoyin daloli zuwa kasuwannin kasashen waje.     

Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta yi zargin cewa kamfanin Emamjomeh ya fitar da dubunnan kayayyaki daga Iran zuwa Pakistan tare da gudanar da hada-hadar kudi na miliyoyin daloli.

Sabon takunkumin dai shi ne irinsa na bakwai da gwamnatin Amurka ta dauka kan Iran tun a ranar 4 ga watan Fabrairu, lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya zartar da dokar yin matsin lamba kan Tehran.

Sabbin takunkuman dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka gudanar da shawarwari guda biyu domin warware sabanin da ke tsakaninsu dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel