Aminiya:
2025-03-03@21:14:41 GMT

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja

Published: 3rd, March 2025 GMT

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya gana da takwaransa na Saliyo Julius Maada Bio a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Ganawar tsakanin shugabannin ƙasashen Afirka biyu ta gudana ne a bayan labule, inda jami’an gwamnati kalilan ne suka halarta.

NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yara

Shugaba Bio ya isa fadar shugaban ƙasa da misalin ƙarfe 12:30 na rana, kuma ya samu tarba daga Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Haka kuma, shugaban na Saliyo ya samu tarba ta ban girma, inda rundunar sojojin shugaban ƙasa suka yi masa fareti tare da kade-kaden gargajiya.

Duk da cewa ba a san ajandar wannan ganawa ba, sai dai Aminiya ta samu cewa ba zai rasa nasaba yunƙurin inganta alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu ba.

Nijeriya da Saliyo mambobi ne na ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka da kuma ƙungiyar tarayyar Afrika, kuma sun haɗa kai kan tsare-tsaren da suka shafi samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a yankin.

Nijeriya ta taka rawar gani wajen ayyukan wanzar da zaman lafiya a ƙasashen Afirka da dama musamman Saliyo.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga

Janar Mai ritaya, tsohon Darakta Janar na NYSC, ya kuɓuta bayan kwana 22 a hannun ‘yan bindiga. Wata majiya ta tabbatar da cewa an sake shi a daren Juma’a, kuma yana karɓar kulawar likita a wani asibitin da ba a bayyana ba saboda dalilan tsaro.

Tsiga ya faɗa hannun ‘yan bindiga ne a ranar 6 ga Fabrairu, 2025, a gidansa da ke ƙauyen Tsiga a ƙaramar hukumar Bakori ta jihar Katsina. Lokacin harin, mutum biyu sun jikkata, yayin da ɗaya daga cikin ‘yan bindigar ya rasa ransa sakamakon harbin da wani daga cikin mutanensa ya yi.

Masu Garkuwa Sun Nemi Fansar Miliyan 250 Kafin Su Saki Tsohon Shugaban NYSC, Janar Tsiga Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Katsina, Sun Sace Tsohon Daraktan NYSC, Janar Tsiga

Har yanzu jami’an gwamnati da hukumomin tsaro, ciki har da rundunar ‘yansandan Katsina, ba su yi tsokaci kan yadda aka sako shi ba. Ana dai hasashen an biya kudin fansa ko an yi wata yarjejeniya domin kuɓutar da shi.

Tsiga ya shiga hannun masu garkuwa ne bayan da miyagun suka mamaye gidansa da makamai. Rahotanni sun bayyana cewa sun kakkarya ƙofofi, lamarin da ya sa tsohon janar ɗin ya fito don fuskantar su, amma suka yi awon gaba da shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya