Faransa Da Burtaniya Sun Ba Da Shawarar Tsagaita Wuta Na Wata Guda A Ukraine
Published: 3rd, March 2025 GMT
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce Paris da London na aiki kan shirin tsagaita wuta na wata guda a Ukraine.
A wata hira da jaridar Le Figaro ta Faransa, Emmanuel Macron ya ce London da Paris suna ba da shawarar tsagaita wuta na wata guda da kuma samar da makamashi.”
Daga baya a cikin jawabin nasa, Macron ya ba da shawarar cewa kasashen Turai su kara yawan kudaden da suke kashewa a fannin tsaro da kashi 3 zuwa 3.
“Tsawon shekaru uku, Rashawa suna kashe kashi 10% na GDPn su a fannin tsaro; Don haka dole ne mu shirya don abin da ke gaba. »
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), Antonio Guterres, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar watan Ramadan, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin mai cike da falala, tausayi, da zaman lafiya.
A sakon da MDD ta fitar ta hannunsa, Guterres ya ce, “Ramadan lokaci ne da ke karantar da kyawawan ɗabi’u na tausayawa, taimakekeniya, karamci, da mutunta juna. Wannan wata dama ce ta ƙara hada kai, sada zumunta, da gina al’umma mai cike da zaman lafiya.”
Ya kuma jaddada muhimmancin tunawa da waɗanda suke cikin hali na ƙunci, musamman ’yan gudun hijira da waɗanda ke fama da rikice-rikice a wurare kamar Gaza, Sudan, da yankunan Sahel.
Guterres ya bayyana damuwarsa kan halin da suke ciki, yana mai cewa, “Ina tare da ku a wannan lokaci mai albarka, kuma ina roƙon samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a gare ku.”
Ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan wata mai alfarma wajen haɗa kai da tabbatar da zaman lafiya.
“Zaman lafiya shi ne ginshiƙin rayuwa, kuma ya kamata mu yi aiki tare don gina duniya mai cike da adalci da mutunta juna,” in ji shi.
Sakatare Janar ɗin ya kuma bayyana cewa a kowanne Ramadan, yana yin azumi tare da al’ummar Musulmi a faɗin duniya, abin da ke ƙara masa fahimtar kyawawan dabi’u na Musulunci da kuma ƙwarin gwiwa.
A karshe, Guterres ya yi fatan Allah Ya karɓi ibadar al’ummar Musulmi yayin da suke azumtar wannan wata mai albarka, yana mai cewa, “Ina taya ku murnar wannan lokaci mai cike da albarka da tausayi.”