Aminiya:
2025-03-03@22:34:57 GMT

An sake naɗa Obasa Kakakin Majalisar Legas

Published: 3rd, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Legas ta sake zaɓar Mudashiru Obasa a matsayin kakakinta bayan Mojisola Meranda ta yi murabus.

Matakin na zuwa ne bayan makonnin da aka shafe ana rikici kan shugabancin majalisar, wanda aka fara bayan tsige Obasa tare da maye gurbinsa da Meranda.

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja

Bayan murabus ɗin nata, nan take ’yan majalisar suka zaɓe ta a matsayin mataimakiyar Obasa, a wani yanayi da ba a saba gani ba a siyasar Nijeriya.

’Yan majalisar sun yabi salon mulkinta da kuma jajircewarta a matsayin mace ta farko kakakin majalisa.

Rahotonni sun ce ta sauka daga muƙamin ne bayan wata ganawa da manyan ’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar game da yadda za a shawo kan rikicin.

Mojisola Meranda dai ta yi murabus daga muƙamin ne bayan shafe kwanaki 49 tana mulki.

Meranda ta hau kujerar kakakin majalisar ne bayan da ’yan majalisar suka tsige Mudashiru Obasa a ranar 13 ga watan Janairu.

Meranda, wacce ta jagoranci zamanta na ƙarshe a yau Litinin, ta sha yabo da jinjina.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Legas Mojisola Meranda

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Jana’izar Shahidan Hizbullah Fiye Da 100 A Kudancin Lebanon

A jiya Juma’a ne dai aka yi jana’izar shahidan Hizbullah 130 a garuruwan Aytas-sha’ab da Aytarun da suke da kudancin Lebanon.

Tashar talabijin din al-manar ta watsa taron jana’izar shahidai 95 da su ka yi shahada watanni uku da su ka gabata a yayin yaki da HKI.

A garin Aytrun da shi ma yake a kudancin Lebanon an yi jana’izar shahidai 35.

Dukkkanin jana’izar biyu ta sami halartar dububan mutane daga cikin garuruwan da kuma wajensu.

 A gefe daya, a daidai lokacin da ake gudanar da jana’izar mutanen a garin Aytatun, sojojin HKI sun kai hari a gefen garin, sai dai babu rahoto akan shahada ko jikkatar mutane.

Dan majalisa mai wakilntar Hizbullah a majalisar dokoki Hassan Fadlallah wanda kuma shi ne shugaban bangaren masu goyon bayan gwgawarmaya a majalisar, ya gabatar da jawabi a wurin jana’izar, inda ya bayyana cewa; Shahidan sun kwanta dama ne a fagen dagar kare daukakar al’ummar Lebanon.

A garin Aytas-sha’ab,  an yi taho mu gama mai tsanani a tsakanin dakarun Hizbullah da sojojin mamayar HKI a lokacin yakin 2006, kuma a wannan yakin ma abinda ya faru kenan,’kamar yadda Fadlallah ya bayyana.

Dan majalisar ya kuma jaddada cewa; Za a sake gina wannan garin, kuma yin hakan nauyi ne da ya rataya a wuyan gwamnatin Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ba za mu binciki Akpabio kan zargin cin zarafin Natasha ba — Majalisar Dattawa
  • Majalisar CPPCC Za Ta Gudanar Da Taron Shekara-shekara Daga Ranar 4 Zuwa Ta 10 Ga Maris
  • An sake zaɓen Obasa Kakakin Majalisar Legas
  • MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza
  • CMG Zai Watsa Bikin Bude Zama Na Uku Na Majalisar CPPCC Karo Na 14
  • Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • An Kaddamar Da Taro Na 10 Na Zaunannen Kwamitin Majalisar CPPCC Karo Na 14
  • An Yi Jana’izar Shahidan Hizbullah Fiye Da 100 A Kudancin Lebanon