Aminiya:
2025-04-23@15:50:57 GMT

An sake zaɓen Obasa Kakakin Majalisar Legas

Published: 3rd, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Legas ta sake zaɓar Mudashiru Obasa a matsayin kakakinta bayan Mojisola Meranda ta yi murabus.

Matakin na zuwa ne bayan makonnin da aka shafe ana rikici kan shugabancin majalisar, wanda aka fara bayan tsige Obasa tare da maye gurbinsa da Meranda.

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja

Bayan murabus ɗin nata, nan take ’yan majalisar suka zaɓe ta a matsayin mataimakiyar Obasa, a wani yanayi da ba a saba gani ba a siyasar Nijeriya.

’Yan majalisar sun yabi salon mulkinta da kuma jajircewarta a matsayin mace ta farko kakakin majalisa.

Rahotonni sun ce ta sauka daga muƙamin ne bayan wata ganawa da manyan ’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar game da yadda za a shawo kan rikicin.

Mojisola Meranda dai ta yi murabus daga muƙamin ne bayan shafe kwanaki 49 tana mulki.

Meranda ta hau kujerar kakakin majalisar ne bayan da ’yan majalisar suka tsige Mudashiru Obasa a ranar 13 ga watan Janairu.

Meranda, wacce ta jagoranci zamanta na ƙarshe a yau Litinin, ta sha yabo da jinjina.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Legas Mojisola Meranda

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ko kun san tanadin da kundin tsarin mulkin ƙasa ya yi game da Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa da ayyukansa da alhakin da ya rataya a wuyansa?

Kundin na tsarin mulkin ƙasa shi ne dai kundin dokoki mafi ƙarfi a Najeriya wanda ya ƙunshi tanade-tanade a kan dukkan al’amuran da suka shafi alhakin da ya rataya a wuyan shugabanni da ma al’ummar ƙasa.

Kuma kamar yadda ya tanadi yadda ake gudanar da dukkan al’amuran ƙasa, haka ya ayyana ƙarfin ikon da kowane shugaba yake da shi, da iyakarsa da ma yadda zai iya miƙa wannan ƙarfin iko ga wani don gudanar da ayyukansa.

NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Shin wanne aiki takamaimai kundin tsarin mulki ya bai wa Mataimakin Shugaban Ƙasa?

Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem