Aminiya:
2025-04-23@15:50:57 GMT

NDLEA ta cafke madugun fataucin miyagun ƙwayoyi bayan shekaru 17 yana ɓuya

Published: 3rd, March 2025 GMT

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) ta bayyana cewa ta kama wani mutum da take zargin madugun fataucin ƙwayoyi ne, Ogbonnaya Kevin Jeff, a maɓoyarsa da ke Jihar Legas.

Sanarwar da mai magana da yawun NDLEA, Femi Baba Femi, ya fitar ta ce kamen mutumin mai shekaru 59 na zuwa ne bayan shafe shekaru 17 yana ɓuya, inda yake fataucin miyagun ƙwayoyi na biliyoyin nairori a faɗin duniya.

Sanarwar ta ambato Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Muhammad Buba Marwa mai ritaya yana bayyana hakan yayin taron manema labarai a Abuja a yau Litinin.

Shugaban NDLEA ya kuma bayyana yadda jami’an sashen ayyukan musamman na hukumar suka riƙa bin diddigin Ogbonnaya biyo bayan nemansa ruwa a jallo da hukumar ’yan sandan duniya INTERPOL ke yi da kuma bayanan sirrin da hukumar leƙen asirin Koriya ta Kudu ta samar a kansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fataucin ƙwayoyi Jihar Legas Ogbonnaya Kevin Jeff

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi ta’aziyya game da rasuwar Paparoma Francis

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya mika ta’aziyya game da  rasuwar shugaban ‘yan darikar katolika na duniya Paparoma Francis.

A wani sako da ya aike a jiya Litinin, Pezeshkian ya ce Paparoma Francis a matsayinsa na shugaban darikar Roman Katolika ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yada koyarwar Yesu Almasihu.

Shugaban ya ce Paparoma ya yi kokari wajen samar da zaman lafiya a duniya, da yekuwar samar da adalci, da ‘yanci, da mu’amala da tsaro a tsakanin addinai.

Daya daga cikin shi ne bayyanannen matsayinsa na yin Allah wadai da kisan gillar da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza da kuma kiran da ya yi na kawo karshen kisan kiyashin da ake yi wa mata da kananan yara Falasdinawan da ba su ji ba ba su gani ba.

A jiya Litini ce Cocin Vatican ta sanar da rasuwar shugaban majami’ar katolika na duniya, Fafaroma Francis yana da shekaru 88 a duniya.

A shekarar 2023 ne cocin ya zabi Fafaroman, wanda asalin sunansa shi ne Cardinal Jorge Mario Bergoglio a matsayin wanda zai jagorance ta, bayan saukar Fafaroma Benedict XVI daga kan mukamin.

Fafaroman ya rasu ne bayan fama da doguwar jinya, inda a baya ya shafe makonni a wani asibiti, inda aka bayyana cewa yana fama da sanyin hakarkari mai tsanani.

Francis, shi ne Paparoma na 266 na Cocin Roman Katolika, kuma an bayyana cewa ya rasu ne sakamakon bugun jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • Iran ta yi ta’aziyya game da rasuwar Paparoma Francis
  • Fadar Vatican Ta Sanar Da Mutuwar Paparoma Francis A Safiyar Yau Litinin
  • Fafaroma Frasncis ya rasu yana da shekaru 88
  • Paparoma Frasncis ya rasu yana da shekaru 88
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama