Leadership News Hausa:
2025-03-04@00:50:24 GMT

Namun Dajin Kasar Sin Sun Karu Yadda Ya Kamata

Published: 4th, March 2025 GMT

Namun Dajin Kasar Sin Sun Karu Yadda Ya Kamata

Hukumar kula da gandun daji da filayen ciyayi ta kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, namun dajin kasar ta Sin sun karu yadda ya kamata ba tare da cikas ba.

Adadin manyan dabbobin Panda ya karu daga kimanin 1,100 a shekarun 1980 zuwa kusan 1,900 a yau, yayin da yawan damisar dusar kankara ya kai fiye da 1,200.

Sai kuma adadin giwayen daji nau’in na Asiya da ya karu daga fiye da 150 zuwa sama da 300.

A fannin shuke-shuke da tsirrai na daji kuwa, an samu nasarar dawo da nau’o’in halittunsu fiye da 200 dake cikin hadarin bacewa bat a duniya, kuma yawancin jinsunansu sun farfado tare da samun kariya yadda ya kamata.

Yau Litinin ne ake tunawa da ranar kare namun daji ta duniya ta shekarar 2025 wadda Majalisar Dinkin Duniya ta ware. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Iran Tana Fuskantar  Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai

Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana cewa; al’ummar Iran tana fuskantar makiya kafirai da munafikai, amma kasar ba ta da matsala da sauran al’ummun duniya.

Har ila yau jagoran ya ce, alkur’ani mai girma yana kunshe da hanyoyin da ya kamata a yi mu’amala da dukkanin wadannan makiyan, da kuma lokacin da ya kamata a yi Magana da su, ko kuma lokacin da ya kamata a zare musu takobi.” Dukkanin wadannan bayanan suna cikin al’kur’ani mai girma.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron karatun alkur’ani mai girma, a jiya Lahadi da dare, ya yi ishara da cutukan ruhi da su ka addabi bil’adama a wannan  zamanin da su ka hada hassada, rowa,mummunan zato, ganda da son kai, da kuma fifita manufa ta kashin kai akan ta al’umma, tare da bayyana cewa, a cikin alkur’ani mai girma da akwai magungunan dukkanin wadannan cutukan.

Jagoran juyin musuluncin ya kuma ce, a bisa mahanga ta musulunci abu na biyu mai muhimmanci bayan tauhidi da ilimi da kyautata alaka da Allah, shi ne shimfida adalci a cikin al’ummar musulmi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Iran Tana Fuskantar  Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai
  • Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Fitaccen Fim Din Na Kasar Sin Mai Suna “Ne Zha 2” Ya Zama Na 7 A Jerin Fina-finai Mafi Samun Kudi A Duniya
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi