Leadership News Hausa:
2025-05-08@10:07:38 GMT

Hasashe Kan Tarukan CPPCC Da NPC Na 2025

Published: 4th, March 2025 GMT

Hasashe Kan Tarukan CPPCC Da NPC Na 2025

Taron kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin (CPPCC) da za a fara ranar 4 ga watan Maris, da na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin (NPC) da za a fara ranar 5 ga watan Maris, su kasance manyan taruka biyu na kasar Sin inda ake gangamin siyasa domin nazartar baya da kuma hangen gaba. Wadannan hukumomi biyu suna karkashin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wadda ke karkashin jagorancin babban sakataren Xi Jinping.

Kwamitin CPPCC na kasa, mai mambobi 2,169, yana aiki ne a matsayin babbar hukumar da ke tafiyar da tsarin dunkulewar sassan kasar ta fuskar siyasa, wanda ke hada kungiyoyin zamantakewa daban daban mashawarta jam’iyyar. Ita kuma, majalisar NPC mai wakilai 2,977, tana aiki ne a matsayin majalisa guda, kuma babbar majalisar dokokin kasar.

Hasashen manazarta kan taruka na bana na da alaka da wani taron karawa juna sani wato “taro kan kamfanoni masu zaman kansu” wanda shugaba Xi ya karbi bakunci a ranar 17 ga watan Fabrairu, wanda ya samu halartar manyan ’yan kasuwa na kasar. A shekarar 2018 ne aka fara gudanar da irin wannan taro da ya kasance na musamman wanda ke kara wa tattalin arzikin kasar karfin gwiwa, musamman bayan dawowar shugaba Trump na Amurka a karo na biyu, wanda ya ayyana kansa a matsayin “sarkin kakaba haraji”, wanda tuni ya sanya karin harajin kashi 10 cikin 100 kan kayayyakin Sin da ke shiga kasarsa. Yanzu, hankalin mahukunta ya karkata kan yadda Sin za ta kara kuzari, da tallafawa kasuwanci da kamfanoni, da kuma mayar da martani ga manufofin cinikayya na Trump.

Ana sa ran tarukan biyu za su bayyana ajandar da za ta kara habaka ci gaba idan aka kwatanta da bara, tare da hasashen kusan kashi 5% na ci gaban GDP, da kashi 4% na GDP na gibin kasafin kudi, da kashi 2% na hauhawar farashin kayayyaki. Bugu da kari, ana sa ran za a samu karin lamuni na kusan yuan tiriliyan 3 daga asusun baitulmali na musamman da kuma yuan tiriliyan 4.5—-5 daga lamuni na musamman na kananan hukumomi. Ta hakan za a gabatar da matakan da za su bunkasa sayayya da karfafa kamfanoni cikin gida masu zaman kansu a fannin kirkire-kirkire. Kazalika, ana sa ran za a tabo batutuwan da suka shafi ci gaban kamfanonin waje masu zaman kansu, da manufofin kasashen wajen musamman wadanda suka shafi batun Taiwan da yadda za a mayar da martani ga hauragiyar Trump. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da kasashen makwabtanta

Shugaban kasar Iran Mas’oud Pezeshkian ya jaddada cewa: “Babban burinsu shi ne neman karfafa hadin kai da ‘yan uwantaka da  makwabtansu, kuma ba su dauke da kiyayya a kansu.”

Shugaba Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a gaban taron majalisar kwararru masu zaben Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran a jiya litinin, ya jaddada wajabcin kiyaye hadin kai da hadin kai a cikin kasar da dukkan al’ummar musulmi. Yana mai cewa: “Tare da haɗin kan kasa, za su iya magance dukkan matsalolin cikin gida.” Sannan ya kuma yi kira da a kaucewa duk wani mataki da zai kawo cikas ga wannan hadin kai tare da daukar hanyar kawo sauyi a maimakon fada da juna.

Shugaba Pezeshkian ya ci gaba da cewa: Al’ummun da ke rayuwa a wannan ƙasar, ko da wane irin ƙabila ne, ko jinsi, ko kuma imaninsu, suna da hakkin gudanar da mu’amala a kan tubalin gaskiya da ‘yancin yin adalci da kuma samun adalci daga gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za Mu Magance Matsalar Ruwan Sha Kafin Ƙarshen 2025 A Kaduna – Uba Sani
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen Ta Ce: Sanarwar Trump Kan Batun Yemen Gazawa Ce Ga Netanyahu
  • Zan Ba Ku $1,000 Kyauta In Zaku Koma Garuruwanku – Trump Ga Baƙin Haure
  • Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei
  • Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus
  • Hannayen jarin kamfanonin fina-finan Amurka sun fadi sakamakon barazanar Trump na kakaba harajin kwastam
  • Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
  • Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah
  • Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma