Aminiya:
2025-04-23@23:36:59 GMT

NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba

Published: 4th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A al’adance, a duk lokacin da watan Ramadana ya ƙarato samari da ’yan mata kan yi musayar kyaututtuka domin kyautata wa juna.

Misali, samari kan haɗa kayan buɗe-baki irinsu madara da ƙwai da sauran kayan maƙulashe da ake yi wa lakabi da ‘Ramadan Basket’ a turance su kai wa ’yan matansu.

Sai dai a wannan shekarar da alamun abin ya sauya salo, domin kuwa ba kamar yadda aka saba ba, kafafen sada zumunta ba su baza hotuna da bidiyon Ramadan Basket ɗin ba.

NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi duba ne kan dalilan da suka hana samari yin ‘Ramadan Basket’ wannan shekarar.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan ramadan basket Ramadan Basket

এছাড়াও পড়ুন:

IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya

Asusun bayar da lamuni na duniya ( IMF) ya yi gargadin cewa rashin tabbataci da Karin kudin harajin Amurka ya haddasa zai iya kawo tsaiko a cikin harkokin cinikiyya ta duniya.

Sanarwar wacce babban jami’in ttatalin arziki na Asusun bayar da lamunin na duniya Pierre -Oliver-Gourinchas, ya bayyana ta kara da cewa; Za a iya samun karuwar hargitsi a cikin harkokin tattalin arzikin na duniya da dama yake fama da matsala.

Jami’in ya yi bayani ne  bayan sake yin hasashe akan ci gaban tattalin arzikin duniya, wanda aka fitar a cikin rahoto a ranar Talatar nan.

Asusun bayar da lamunin ya yi hasashen cewa tattalin arzikin duniyar zai bunkasa da kaso 2.8 % a cikin 2025, da hakan yake nuni da koma baya mai tsanani da ya kai 0.5, idan aka kwatantan da hasashen da ya yi a baya a watan Janairu.

Bayan da Amurka ta sanar da Karin kudaden fito akan kayan kasuwanci da ake shigar mata daga kasashen mabanbanta, cibiyoyin kudi na duniya sun yi hasashe, tare da nuni da cewa za a sami koma baya a ci gaban tattalin arzikin na duniya.

Rahoton ya kuma yi gargadi akan  dagula kasuwanci, da hakan zai iya haddasa tsaiko na ci gaba, ko ma haddasa sauyi a hada-hadar kudade.

 Asusun bayar da lamunin na duniya ya yi kira ga kasashe da su bude tattaunawa a tsakaninsu, su kuma samar da daidaito a cikin dokokin kasuwanci, da kiyaye ‘yancin da hada-hadar kudade suke da shi, saboda karfafa tattalin arzikin duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno