Aminiya:
2025-03-04@08:31:18 GMT

NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba

Published: 4th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A al’adance, a duk lokacin da watan Ramadana ya ƙarato samari da ’yan mata kan yi musayar kyaututtuka domin kyautata wa juna.

Misali, samari kan haɗa kayan buɗe-baki irinsu madara da ƙwai da sauran kayan maƙulashe da ake yi wa lakabi da ‘Ramadan Basket’ a turance su kai wa ’yan matansu.

Sai dai a wannan shekarar da alamun abin ya sauya salo, domin kuwa ba kamar yadda aka saba ba, kafafen sada zumunta ba su baza hotuna da bidiyon Ramadan Basket ɗin ba.

NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi duba ne kan dalilan da suka hana samari yin ‘Ramadan Basket’ wannan shekarar.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan ramadan basket Ramadan Basket

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres na mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Ramadan yana kunshe da dabi’u na tausayi, tausayawa da karamci. Sannan dama ce ta sake haduwa da dangi da sauran al’umma.

Kazalika dama ce ta tuna wadanda ba su samu damar sake ganin watan ba. Ga duk wadanda suka samu ganin wannan lokaci mai tsarki cikin halin gudun hijira da tashin hankali, ina so in bayyana sakon tausayawa a gare su.

Ina goyon baya ga duk wadanda ke cikin halin tsanani da wahala, tun daga Gaza da sauran yankuna, zuwa Sudan, Sahel da sauran su. Kuma ina mai ba da hadin kai da masu gudanar da Azumin watan Ramadan da yin kira ga zaman lafiya da mutunta juna. A duk watan Ramadan, na kan kai ziyarar hadin kai tare da yin Azumi tare da al’ummar Musulmi a fadin duniya.

 Wadannan ayyuka suna tunatar da duniya hakikanin fuskar Musulunci. Kuma ko da yaushe na kan zama mafi samun kwarin gwiwa da kwanciyar hankali a wannan lokaci.

A cikin wannan wata mai alfarma, dukkkanmu muna samun daukaka ta hanyar dabbaka wadannan dabi’u kuma muna rungumar ‘yan uwantaka don gina duniya mai adalci da zaman lafiya ga kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Haska Fim Din Sin A Sinimomin Najeriya Da Ghana Da Laberiya
  • Ramadan: Coci ya ciyar da Musulmi 1,000 a Kaduna
  • MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
  • NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?
  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • A Yau Ce Dokar Haramta Amfani Da Tankunan Mai Masu Daukar Lita 60,000 A Najeriya