Aminiya:
2025-04-27@22:29:29 GMT

Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba

Published: 4th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana mutane zuwa kwasar man fetur daga wata tankar mai da ta yi hatsari a Jalingo, hedikwatar Jihar Taraba.

A safiyar ranar Litinin ne ’yan sanda da jami’an hukumar tsaro ta Sibil Difens (NSCDC), suka ɗauki wannan mataki bayan faɗuwar tankar man a kan babban hanyar Jalingo zuwa Wukari.

Rahotanni sun bayyana cewa faɗuwar tankar man ke da wuya, jami’an tsaron suka isa wurin, inda suka killace wurin domin hana mutane kaiwa inda man yake.

Daga nan ɗauke tankar man da babbar motar ɗauko, aka mayar  wata motar sannan aka tafi da ita.

NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba NDLEA ta cafke madugun fataucin miyagun ƙwayoyi bayan shekaru 17 yana ɓuya

Kakakin Hukumar NSCDC ne jihar, SC Sam Illiya, ya bayyana wa wakilinmu cewa kwamandan hukumar na jihar da kansa ya jagoranci jami’ansa zuwa wurin domin gudanar da aikin.

Kakakinn ’yan sanda na jihar, SP Usman Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Kwasar man fetur Tankar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Tabbatar Da Aniyar Gwamnatinsa Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro

”Wannan lokaci ne na bakin ciki, kuma a cikin irin wadannan lokutan ne kuka san wadanda ke kulawa da ku da gaske.”

 

Ribadu ya bayyana cewa Gwamnatin Bola Tinubu ta gaji tashin hankali da ke fama da shi a kasar nan, kuma tana aiki tukuru don gyara abubuwan da suka lalace.

 

Ya ce, “Na zo nan ne don in jajanta muku da sauran mutanen kirki na Benuwai kan asarar rayuka da aka yi da kuma tabbatar muku da cewa muna tare da ku.

 

“Benuwai jiha ce mai matukar muhimmanci a Nijeriya. Ta kasance daya daga cikin jihar da ake samar da abinci a kasa, ita ce ta farko wurin samar da abinci, kuma muna alfahari da hakan.

 

“Za mu magance wannan matsalar. Ka ku kadai ku ce jin zafin ba, wannan kalubalen ya shafi mu duka. Lokacin da ibtila’i ta zo, mutanen kirki dole ne su hadu don fuskantar ta.

 

“Sojojinmu da hukumomin tsaro suna yin iya bakin kokarinsu, amma irin wannan lamarin yana ci gaba da faruwa ne saboda ba zai yiwu a tura jami’an tsaro zuwa kowane kauye ba.

 

“Kasashe suna fuskantar mawuyacin hali. Rashin tsaro kalubale ne mai wuyan shawowa.

 

“Haifar da tashin hankali abu ne mai sauki, amma warware matsalolin da ke tattare da su ya fi wahala, duk da haka muna yin iya bakin kokarinmu.

 

“A matsayinmu na gwamnatin da ba ta cika shekaru biyu ba, mun riga mun rage yawan tashin hankalin da muka gada.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano
  • Gobara A Haramtacciyar Wurin Ajiye Man Fetur Ta Ci Rayukan Mutane 5 A Jihar Ribas
  •  Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
  • Zanga-zangar Lumana Wani Bangare Ne Na Mulkin Dimokuradiyya
  • Tuƙin Ganganci: Direba Ya Kashe Jami’in KAROTA
  • Tinubu Ya Tabbatar Da Aniyar Gwamnatinsa Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro
  • ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa