A wani rahoto wanda ba’a tantance ba kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kawayenta a wajen kungiyar OPEC +  za su kara yawan man fetur da suke haka da ganga 138,000 a cikin watan Afrilu mai zuwa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wasu majiyoyin kungiyar wadanda ba’a bayyana ba suna cewa kungiyar OPEC + bata kara yawan man da take haka ba na lokaci mai tsawo, amma a halin yanzu zata kara kamar yadda aka sanar.

Labarin ya kara da cewa kungiyar tana rage ganga miliyon 5.85 wanda kuma shi ne kashi 5.7%  na yawan man da ake haka a duniya, wannan kuma ya yi dai dai da shawarar da OPEC + suka dauka tun shekara ta 2022.

Labarin ya kara da cewa kasashen kungiyar sun amince da haka daga ciki har da kasar Rasha kasar da ta fi ko wace kasa hakar mai a duniya.

Akwai jitajitan cewa Amurka zata kara takurawa Iran a cikin watanni masu zuwa, amma Iran ta ce hakan ba zai shafi ta ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sakataren MDD Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Biya Rabonsu Na Kudaden Tsaron Kasa Da Kasa

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa karfin bangaren sojojin tabbatar da zaman lafiya na majalisar a duniya, yana dai dai da karfin dukkan kasashen da suke bawa kudaden da ake tafiyar da ayyukansu ne. Don haka ya bukaci kasashen da basu biya rabonsu na kudade karo-karon da ake yi don tafiyar da ayyulan zaman lafiya a duniya bas u yi hakan da gaggawa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto babban sakataren yana fadar haka a jiya talata ya kuma kara da cewa a halin yanzu majalisar tana tafiyar da ayyukan zaman lafiya har 11 a kasashen duniya  wadanda suka hana da  nahiyar Afirka Asia da kuma turai. Guterres ya kara da cewa majalisar tana da sojojin tabbatar da zaman lafiya a kasashen  Congo, Afirka ta tsakiya, Sudan ta Kudu, Lebanon, Cyprus da kuma Kosovo.

Ya ce abinda ake bukata don tafiyar da 9 daga cikin ayyukan tabbatar da zaman lafiya 11 da Majalisar take da su, ya kai dalar Amurka billiyon $5.6 wanda yayi kasa da kasha 8.2% na abinda ta kashe a shekarar da ta gabata.

Labarin ya kara da cewa dukkan kasashen duniya 193,  mambobi a MDD  suna da abinda aka ware mata na kudaden da zata gabatar saboda tabbatar da zaman lafiya a duniya. Guterres ya kammala da cewa MDD ce take gaba a ayyukan tabbatar da zaman lafiya a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Kasashen Turai uku wato E3 Zasu Bude Tattaunawa A Tsakaninsu A Birnin Istambul A Gobe Jumma’a
  • Ma’aikatar Harkokin wajen kasar Iran Ta Yi Watsi da Zargin Trump
  • Iran Da Japan Sun Kara Zurfafa Dankon Zumunci Da Ke Tsakaninsu
  • Babban Sakataren MDD Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Biya Rabonsu Na Kudaden Tsaron Kasa Da Kasa
  • Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
  • Iran: Babban Kwamandan Sojojin Ruwa Na JMI Yace Sojojinsa A Shirye Suke Su Shiga Yaki Da Makiya
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Gaza
  • Shugaban Kungiyar Hizbulla Ya Ce Cewa Kungiyarsa Ba Zata Taba Mika Kai Ga Bukatun HKI Ba
  • Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
  • Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a