OPEC Da Kawayenta Zasu Kara Yawan Man Da Suke Haka A Karon Farko Tun Shekara Ta 2022
Published: 4th, March 2025 GMT
A wani rahoto wanda ba’a tantance ba kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kawayenta a wajen kungiyar OPEC + za su kara yawan man fetur da suke haka da ganga 138,000 a cikin watan Afrilu mai zuwa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wasu majiyoyin kungiyar wadanda ba’a bayyana ba suna cewa kungiyar OPEC + bata kara yawan man da take haka ba na lokaci mai tsawo, amma a halin yanzu zata kara kamar yadda aka sanar.
Labarin ya kara da cewa kungiyar tana rage ganga miliyon 5.85 wanda kuma shi ne kashi 5.7% na yawan man da ake haka a duniya, wannan kuma ya yi dai dai da shawarar da OPEC + suka dauka tun shekara ta 2022.
Labarin ya kara da cewa kasashen kungiyar sun amince da haka daga ciki har da kasar Rasha kasar da ta fi ko wace kasa hakar mai a duniya.
Akwai jitajitan cewa Amurka zata kara takurawa Iran a cikin watanni masu zuwa, amma Iran ta ce hakan ba zai shafi ta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Sakataren MDD Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Biya Rabonsu Na Kudaden Tsaron Kasa Da Kasa
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa karfin bangaren sojojin tabbatar da zaman lafiya na majalisar a duniya, yana dai dai da karfin dukkan kasashen da suke bawa kudaden da ake tafiyar da ayyukansu ne. Don haka ya bukaci kasashen da basu biya rabonsu na kudade karo-karon da ake yi don tafiyar da ayyulan zaman lafiya a duniya bas u yi hakan da gaggawa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto babban sakataren yana fadar haka a jiya talata ya kuma kara da cewa a halin yanzu majalisar tana tafiyar da ayyukan zaman lafiya har 11 a kasashen duniya wadanda suka hana da nahiyar Afirka Asia da kuma turai. Guterres ya kara da cewa majalisar tana da sojojin tabbatar da zaman lafiya a kasashen Congo, Afirka ta tsakiya, Sudan ta Kudu, Lebanon, Cyprus da kuma Kosovo.
Ya ce abinda ake bukata don tafiyar da 9 daga cikin ayyukan tabbatar da zaman lafiya 11 da Majalisar take da su, ya kai dalar Amurka billiyon $5.6 wanda yayi kasa da kasha 8.2% na abinda ta kashe a shekarar da ta gabata.
Labarin ya kara da cewa dukkan kasashen duniya 193, mambobi a MDD suna da abinda aka ware mata na kudaden da zata gabatar saboda tabbatar da zaman lafiya a duniya. Guterres ya kammala da cewa MDD ce take gaba a ayyukan tabbatar da zaman lafiya a duniya.