Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
Published: 4th, March 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaei ya yi kira ga gwamnatin kasar Turkiya ta sake tunani kan kalamanta dangane da JMI.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei ya na fadar haka a jiya Litinin, a taron mako mako da ya saba gabatarwa a ko wace litinin. Ya yi wannan kiran ne bayan wata maganan da ministan harkokin wajen kasar Turkiyya Hakan Fidan ya yi dangane da kasar Iran.
Labarin ya kara da cewa, Hakan Fiddan ya bayyana cewa shirye-shiryen JMI a kasar Siriya masu rusa kasar ne, kafin juyin mulkin da Turkiyan ta dauki nauyinsa a baya-bayan nan a kasar Siriya.
Ya ce: Fidan yana magana kan gagarumin taron Jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasaralla wanda aka gudanar a birnin Beirut na kasar Lebanon a ranar Lahadi 23 ga watan Fabrairun da ta gabata. Tare da halattar manya-manyan jami’an gwamnatin kasar.
Baghaei ya ce: Ministan yana nufin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya kai zuwa taron na Jana’iza da ganawar da yayi da Jami’an gwamnatin kasar Lebanon a lokacin, da zuwan sa Geneva inda ya halarci taron kwance damarar makaman Nukliya, da kuma ganawarsa da ministocin harkokin wajen kasashen Indonasia, Bahrain, Kuwait da kuma wasu a gefen taron.
Ya ce Iran tana maganar a dai dogaro da manya-manyan kasashen duniya, kuma kasashen yankin su magance matsalolinsu da kansu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gabatar Da Tayin Shiga Tsakanin Don Sasanta Indiya Da Pakisatan
A dai-dai lokacinda kasashen Indiya da Pakisatn suke tada jijiyoyin wuta kan wani harin ta’addanci da ya kai ga mutuwar mutane 27 masu yawon shakatawa a yankin Kashmir na kasar Indiya, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gabatar da tayin shiga tsakani don dai-daita tsakanin kasashen biy.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka, a shafinsa na X, ya kuma kara da cewa Iran tana da dangantaka mai karfi tsakaninta da kasashen biyu, kuma makobta ne kuma yan uwa wadanda suke da tsohuwar dangantaka ta al-adu a tsakaninsu na karnuka, ba za muyi kasa a guiwa wajen sasantasu ba, idan sun bamu wannan damar.
A cikin makon da ya gabata ne wasu yan bindiga suka bude wuta kan wasu maso yawan shakatawa a yankin Kashmir na kasar Iran inda mutane 27 suka mutu. Gwamnatin Undiya tana zargin Pakistan da hannu dumu-dumu a cikinsa, a yayinda gwamnatin kasar Pakisatan ta musanta hakan ta kuma yi allawadai da harin. Amma ta kara da cewa idan indiya ta kuskura ta yi amfani da makami a kanta to zata rana.
A daren jamm’an da ta gabata dai bangarorin biyu sun kai ga musayar wuta a tsakaninsu a kan iyakokin kasashen biyu.
Ministan ya bayyana cewa kasar zata yi amfani da ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Islamabad da kuma New Delhi don shiga tsakanin su idan sun amince da hakan.
Kasashen indiya da Pakistan dai sun dade suna takaddama kan mallakar Yankin Kashmir kuma sun sha shiga yaki saboda hakan.