HausaTv:
2025-03-04@10:09:08 GMT

Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran

Published: 4th, March 2025 GMT

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaei ya yi kira ga gwamnatin kasar Turkiya ta sake tunani kan kalamanta dangane da JMI.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei ya na fadar haka a jiya Litinin, a taron mako mako da ya saba gabatarwa a ko wace litinin. Ya yi wannan kiran ne bayan wata maganan da ministan harkokin wajen kasar Turkiyya Hakan Fidan ya yi dangane da kasar Iran.

Labarin ya kara da cewa, Hakan Fiddan ya bayyana cewa shirye-shiryen JMI a kasar Siriya masu rusa kasar ne, kafin juyin mulkin da Turkiyan ta dauki nauyinsa a baya-bayan nan a kasar Siriya.

Ya ce: Fidan yana magana kan gagarumin taron Jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasaralla wanda aka gudanar a birnin Beirut na kasar Lebanon a ranar Lahadi 23 ga watan Fabrairun da ta gabata. Tare da halattar manya-manyan jami’an gwamnatin kasar.

Baghaei ya ce: Ministan yana nufin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya kai zuwa taron na Jana’iza da ganawar da yayi da Jami’an gwamnatin kasar Lebanon a lokacin, da zuwan sa Geneva inda ya halarci taron kwance damarar makaman Nukliya, da kuma ganawarsa da ministocin harkokin wajen kasashen Indonasia, Bahrain, Kuwait da kuma wasu a gefen taron.

Ya ce Iran tana maganar a dai dogaro da manya-manyan kasashen duniya, kuma kasashen yankin su magance matsalolinsu da kansu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

OPEC Da Kawayenta Zasu Kara Yawan Man Da Suke Haka A Karon Farko Tun Shekara Ta 2022

A wani rahoto wanda ba’a tantance ba kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kawayenta a wajen kungiyar OPEC +  za su kara yawan man fetur da suke haka da ganga 138,000 a cikin watan Afrilu mai zuwa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wasu majiyoyin kungiyar wadanda ba’a bayyana ba suna cewa kungiyar OPEC + bata kara yawan man da take haka ba na lokaci mai tsawo, amma a halin yanzu zata kara kamar yadda aka sanar.

Labarin ya kara da cewa kungiyar tana rage ganga miliyon 5.85 wanda kuma shi ne kashi 5.7%  na yawan man da ake haka a duniya, wannan kuma ya yi dai dai da shawarar da OPEC + suka dauka tun shekara ta 2022.

Labarin ya kara da cewa kasashen kungiyar sun amince da haka daga ciki har da kasar Rasha kasar da ta fi ko wace kasa hakar mai a duniya.

Akwai jitajitan cewa Amurka zata kara takurawa Iran a cikin watanni masu zuwa, amma Iran ta ce hakan ba zai shafi ta ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • OPEC Da Kawayenta Zasu Kara Yawan Man Da Suke Haka A Karon Farko Tun Shekara Ta 2022
  • Masar : Za’a Gabatar Da Shirin Baiwa Falasdinawa Yancin Zama A Kasarsu
  • Kwance Damarar Dakarun Hashdu Zai Ragewa Harkokin Tsaron Kasar Iraki Aminci
  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
  • Kasar Masar Ta Tabbatrawa Falasdinawa, Tana Bayansu Kafin Taron Kasashe Larabawa
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu