HausaTv:
2025-04-06@15:45:16 GMT

Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran

Published: 4th, March 2025 GMT

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaei ya yi kira ga gwamnatin kasar Turkiya ta sake tunani kan kalamanta dangane da JMI.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei ya na fadar haka a jiya Litinin, a taron mako mako da ya saba gabatarwa a ko wace litinin. Ya yi wannan kiran ne bayan wata maganan da ministan harkokin wajen kasar Turkiyya Hakan Fidan ya yi dangane da kasar Iran.

Labarin ya kara da cewa, Hakan Fiddan ya bayyana cewa shirye-shiryen JMI a kasar Siriya masu rusa kasar ne, kafin juyin mulkin da Turkiyan ta dauki nauyinsa a baya-bayan nan a kasar Siriya.

Ya ce: Fidan yana magana kan gagarumin taron Jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasaralla wanda aka gudanar a birnin Beirut na kasar Lebanon a ranar Lahadi 23 ga watan Fabrairun da ta gabata. Tare da halattar manya-manyan jami’an gwamnatin kasar.

Baghaei ya ce: Ministan yana nufin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya kai zuwa taron na Jana’iza da ganawar da yayi da Jami’an gwamnatin kasar Lebanon a lokacin, da zuwan sa Geneva inda ya halarci taron kwance damarar makaman Nukliya, da kuma ganawarsa da ministocin harkokin wajen kasashen Indonasia, Bahrain, Kuwait da kuma wasu a gefen taron.

Ya ce Iran tana maganar a dai dogaro da manya-manyan kasashen duniya, kuma kasashen yankin su magance matsalolinsu da kansu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu

Dubun-dubatar al’ummar kasar Aljeriya sun gudanar da wani gagarumin gangami da jerin a wannan Juma’a a birnin Algiers babban birnin kasar, domin yin Allawadai da laifukan yaki da Haramtacciyar Kasar Isra’ila take aikatawa a kan al’ummar yankin zirin Gaza.

Kamar yadda kungiyar Movement of Society for Peace ta yi kira, dubban  ‘yan kasar Aljeriya ne suka fito domin nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu a gaban hedikwatar jam’iyyar da ke unguwar  al-Mouradia, babban birnin kasar Aljeriya.

Sai dai hukumomin Aljeriya sun kewaye masu zanga-zangar don hana fadada zanga-zangar zuwa wuraren da jama’a ke taruwa.

Masu zanga-zangar sun yi ta rera taken nuna rashin amincewarsu da kisan kiyashin da “Isra’ila” ke yi a Gaza, inda suka yi Allah wadai da saka al’ummar Gaza a cikin yunwa da kuma ci gaba da aiwatar da  kashe-kashen da Isra’ila ke yi, da nufin tilasta wa al’ummar Palasdinu kauracewa gidajensu da yankunansu . Masu zanga-zangar sun kuma yi kira da a rufe ofishin jakadancin Amurka da ke Aljeriya, saboda rawar da Amurka ta take takawa wajen mara wa Isra’ila baya ga laifukan Isra’ila a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha za ta bude ofishin jakadanci a Nijar nan ba da jimawa ba
  • Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu
  • APC Ce Ke Min Bita-Da-Ƙulli Wajen Yi Min Kiranye – Sanata Natasha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Fadawa Muhammad Bin Salman Kan Cewa Tehran Tana Shirin Kare Kanta
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Kudurin Da Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD Ta Amince A Kanta
  • Ministocin harkokin wajen kasashen AES na gana da Rasha
  • Xi Ya Jaddada Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Kyakkyawar Kasar Sin 
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Gyara Kuskurenta Na “Kakaba Haraji Ramuwar Gayya”
  • Rasha ta gargadi Amurka kan duk wani gigin ka wa kasar Iran hari
  • Aljeriya ta bukaci taron gaggawa a kwamitin tsaro kan Falasdinu