Aminiya:
2025-04-25@05:50:11 GMT

Miji ya yi yunƙurin kashe matarsa kan zargin maita

Published: 4th, March 2025 GMT

Kotu ta tsare wani magidanci a gidan yari kan zargin barazana ga rayuwar matarsa da yake zargin ta da maita.

Babbar Kotun Musulunci da ke Gazawa a Jihar Kano ta tsare mutumin ne bayan ya yi barazana tare da yunƙurin kai wa matar tasa farmaki da adda.

Mai gabatar da ƙara, Sadiq Yusuf ya shaida wa kotun cewa mutumin ya yi yunƙurin aika-aikan ne bisa zargin matarsa da kama kuruwar ɗansu da ya jima yana fama da rashin lafiya.

Magidancin da ke zaune a ƙauyen Gawo da iyalin nasa ya musanta tuhumar da ake masa, don haka, Alƙali Nura Ahmad ya ba da umarnin tsare shi a gidan yari.

Bidiyon batsa: Kotu ta ɗaure ’yan Tiktok a gidan yari a Kano NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba

Ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 20 ga watan nan na Maris domin masu ƙara su gabatar da shaidu.

Ɓari: Matan aure sun yi wa wata barazana

A wata sabuwa kuma, an gurfanar da wasu matan aure biyu kan zargin yin barazana ga wata da suke zargi da haddasa zubewar juna biyun dayarsu.

Kotun da ke zamanta a unguwar Danbare, Ƙaramar Hukumar Kumbotso, na zargin matan auren da haɗa baki da yunƙurin aikata laifi.

Ana zargin matan waɗanda mazauna unguwar Rimin Auzinawa da ke Ƙaramar Hukumar Ungogo da barazanar ga matar tare da zargin ta da haddasa zubewar juna biyun dayarsu.

Sai dai sun musanta zargin, inda daga baya alƙalin, Khadi Munzali Idris Gwadabe, ya ba da belinsu, bayan lura da yanayin lafiyar wadda ta yi ɓarin, da ke murmurewa.

Ya kuma daga sauraron shari’ar zuwa ranar 16 watan Afrilu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matar zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta

Munanan azabtarwa kan fursunonin Falasdinawa a gidajen kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila da suka hada da fyade da dangogin azaba

Rahoton da Hukumar Kula da Fursunoni Falasdinawa dakungiyar Fursunonin Falasdinawa da aka saka daga gidan kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila sun fiyar da rahoton hadin gwiwa a yau Alhamis, 24 ga watan Afrilun shekara ta 2025, da ya kunshi munanan shaida daga fursunonin Zirin Gaza da ke tsare a gidan yarin Negev da sansanin Ofer na gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila.

Rahoton ya bayyana yadda ake ci gaba da yin fyade da cin zarafi ga wadanda ake tsare da su a Gaza.

Wanda ake tsare da shi a sansanin Ofer ya bayyana cewa da gangan masu gadin sansanin suke kara radadin yadda wanda ake tsare da su da hakan ke kara masifar azabtarwar da ake gana musu. Haka kuma wanda ake tsare ana yi masa fyade a gaban ’yan uwansa da ake tsare da su, da nufin wulakanta shi da kuma rusa tunaninsa, da hakan ke kara tsoro da firgici a tsakanin sauran wadanda ake tsare da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Ƙasashen AES sun kafa gidan rediyo don yaƙar farfagandar turawa
  • An daƙile yunƙurin juyin mulki a Burkina Faso
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran