HausaTv:
2025-04-24@18:27:37 GMT

Trump Ya Dakatar Da Taimakon Da Kasarsa Take Bai Wa Ukiraniya

Published: 4th, March 2025 GMT

Kafafen watsa labarun Amurka sun ambaci cewa, shugaban kasar Donald Trump ya bayar da umarnin dakatar da duk wani taimako na soja da ake bai wa Ukirnaiya, daga ciki har da makaman da ake kai wa ta sama da jiragen ruwa da kuma wadadna  a halin yanzu sun isa kasar Poland.

Jaridar “Bloomberg” ta bayyana cewa; bayan kwanaki kadan da aka yi cacar baki a tsakanin shugaban na Amurka Donald Trump da kuma takwaransa na Ukiraniya  Volodymyr Zelensky, shugaban na kasar Amurka ya bayar da umarnin a dakatar da bai wa Ukiraniya duk wani taimako na soja.

Wani jami’i a ma’aikatar tsaron Amurka ya bayyana cewa;               “ Amurkan ta dakatar da duk wani taimako na soja da take bai wa Ukiraniya a halin yanzu, har zuwa lokacin da shugabannin kasar za su nuna cewa da gaske suna son zaman lafiya.”

Ita kuwa jaridar “Washington Post” ta nakalto cewa, jami’an gwamnatin Amurkan suna kuma nazarin yadda za su dakatar da musayar bayanai da suke yi da Ukiraniya, haka nan horon soja da ake ba su.”

A ranar juma’ar da ta gabata ne dai shugaban kasar Ukiraniya Volodymyr Zelensky ya kai ziyara Amurka, sai dai ba ta kare da dadi ba a tsakaninsa da shugaban kasar Donald Trump, saboda sabanin da su ka samu akan batun tsagaita wutar yaki da kuma yarjejeniya akan ma’adanai.

Trump ya zargi shugaban na Ukiraniya da kokarin kunna wutar yakin duniya na 3,alhali bai taki wani abu ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-haren a kan biranen San,a,Sa’adah da kuma Hudaidah na kasar Yemen.

Kamfanin dillancin labarun “Saba’a” na kasar Yemen ya nakalto cewa sojojin na Amurka sun kai hare-hare har sau uku a dutsen Naqam, wanda  yake gabashin birnin San’aa.

Kamfanin dillancin labarun na “Saba’a” ya kuma ce, jiragen yakin Amurka din sun kai hare-haren ne a tsakanin marecen jiya Laraba da kuma safiyar yau Alhamis.

Daga cikin wuraren da aka kai wa harin jiya da marecen da akwai Sahlin dake karamar hukumar Ali-Salim. Sau 6 Amurkan ta kai wa yankin hare-hare.

Da safiyar yau Alhamis kuwa jiragen yakin na Amurka sun kai hare-hare a gundumar Sa’adah.

Wasu yankunan da su ka fuskanci hare-haren su ne, al-tahita, dake kudancin gundumar Haudaidah, a yammacin kasar ta Yemen.

Amurka tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda  bayar da kariya ga HKI, da zummar hana Yemen kai hare-hare akan manufofin ‘yan sahayoniya a ruwan tekun ” Red Sea”.

Kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta bayyana cewa ba za ta taba daina kai wa HKI hare-haren ba har sai idan an daina kai wa Gaza hari. Bugu da kari ta sanar da cewa;za ta ci gaba da hana jiragen ruwa wucewa ta tekun “Red Sea” har zuwa lokacin da za a kawo karshen hana shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Burkina Faso ta sanar da dakile wani yunkurin juyin mulkin a kasar
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis