RAMADAN: Gwamnatin Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar
Published: 4th, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya amince da rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnati a Jihar Jigawa yayin azumin Ramadan na 2025.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar kuma aka rabawa manema labarai aDutse, wacce Babban Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya sanya wa hannu.
“Farawa daga yanzu, ma’aikatan gwamnati a jihar za su rika fara aiki da karfe 9:00 na safe kuma su tashi da karfe 3:00 na yamma daga Litinin zuwa Alhamis, raguwar awanni biyu daga tsohon lokacin rufewa na karfe 5:00 na yamma.
Babban Sakataren ya bayyana cewa an yi hakan ne domin baiwa ma’aikatan gwamnati damar shiryawa azumin Ramadan da kuma gudanar da ibadu cikin sauki a wannan wata mai alfarma.
“An yi fatan cewa ma’aikatan gwamnati za su yi amfani da wannan lokaci don yin addu’o’i domin samun shiriya da albarka ga jiharmu,” in ji shi.
Alhaji Muhammad Dagaceri ya kara da cewa ana sa ran ma’aikatan za su yi amfani da lokacin azumi wajen yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki ga jihar da kasa baki daya.
END/ USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ma aikatan Jihar Rage
এছাড়াও পড়ুন:
Motocin Buldoza Suna Ta Rusa Gidajen Falasdinawa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
Kungiyar Hamas ta bada sanarwan cewa gwamnatin HKI a yankin yamma da Kogin Jordan tana rusa gidajen Falasdinawa a sansanin yan gudun hijira na Nur- Ashamsh, a ranar farko ta watan Ramadan mai alfarma.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Nihad Ashawish shugaban kwamitin mai kula da sansanin yan gudun hijirar yana fadar haka a jiya Asabar ya kuma kara da cewa a jiya Asabar ce motocin Buldoza na HKI suka shiga unguwar Almanshiya suka rusa gidajen wasu Falasdinawa, sannan suka bata hanyoyi a unguwar.
Kamfanin dillancin labaran Abadulu na kasar Turkiya ya nakalti Ashawish yana cewa, sojojin HKI su kan tilastawa Falasdinawa fita daga gidajensu sannan su rusasu a gabansu. Tare da umurnin su fice daga yankin su je inda suka ga dama.
Hamas ta kammala da cewa da wannan aikin zamu fahinci cewa gwamnatin HKI tana son kara korar Falasdinawa daga kasarsu, musamman daga yankin yamma da kogin Jordan.
Kungiyar ta bukaci MDD ta dauki matakan da suka dace don hana yahudawan mamayar karin gidajen Falasdinawa a arewacin yankin yamma da Kogin Jordan.
A jiya Asabar kwanaki 21 cur Kenan gwamnatin HKI take rurrusa gidaje da lalata hanyoyi a garuwan Falasdinawa dake yankin yamma da kogin Jordan musamman garuruwan Tulkaram, da Jenin.
Majiyar asbitoci a yankin yamma da kogon Jordan sun bayyana cewa daga lokacin zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa 64 sannan wasu dubbai an koresu daga gidajensu.