HausaTv:
2025-03-04@17:52:53 GMT

Za’a yi Garambawul Kan Dokar Amfani Da Shafukan Sada Zumunta A Kasar Nijer

Published: 4th, March 2025 GMT

Gwamnatin jamhuriyar  Nijar ta bayyana aniyarta ta yin garambawul ga dokar tsarin amfani da shafukan sada zumunta irin su Whatsapp da Facebook da dai sauransu  a kasar.

Ministan sadarwa na kasar Nijer sidi Mohammad Raliyu shi ne ya bayyana hakan, yana me cewa duk wani zaure na Whattsapp ko Facebook da ya kunshi mutanen  50 zuwa 100 dole ne yayi rajista a wajen hukuma don ci gaba da aikinsa.

Ministan ya ce zaurukan whattsap da Facebook na zama hanyoyin kasuwanci da kuma yaƙar gwamnatoci,  wannan yasa za ta bullon da sabon shiri tare da  wasu ƙasashen Afirka domin sake duba dokar da ta bada damar aiki da shafukan sada zumunta a Kasashen,  domin dakile amfani da ita ta hanyar da bata dace ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi

‘Yan majalisar dokokin kasar Iran sun kada kuri’ar tsige ministan harkokin tattalin arziki da kudi Abdonnasser Hemmati daga mukaminsa saboda matsalolin tattalin arziki da kuma faduwar darajar kudin kasar.

Hemmati ya rasa kuri’ar amincewa a zaman majalisar na wannan Lahadi inda ‘yan majalisa 182 daga cikin 273 suka kada kuri’ar tsige shi. ‘Yan majalisa tamanin da tara ne suka bukaci ya ci gaba da zama a kan mukaminsa.

A yayin Zaman ministan da kansa da shugaban kasar Masoud Pezeshkian sun halarci wurin, yayin da kuma ‘yan majalisar kan batun kudurin, amma dai kudirin ya wuce bayan samun rinjayen amincewa da shi.

Shugaba Pezeshkian ya kare Hemmati, tsohon gwamnan babban bankin kasar Iran, ya kuma ce kasar na cikin yakin tattalin arziki da makiya, kuma zargin juna ba zai magance wata matsala ba.

Ya jaddada cewa hadin kai da hadin gwiwa ne kadai mafita ga matsalolin da kasar ke fuskanta.

Hemmati ya kuma yi jawabi a zaman inda ya ce Iran na da karfin iko kuma za ta yi nasara a yakin tattalin arzikin makiya.

Wasu gungun ‘yan majalisa 91 ne suka fara shirin tsige Hemmati, saboda gazawarsa wajen daidaita kasuwanni da kuma dakile hauhawar farashin kayayyaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Junbilat: ‘Yan Sahyoniya Suna Son Tarwatsa Kasar Syria
  • An Fara Amfani Da Dandalin Samar Da Bayanai Na Kasar Sin
  • Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
  • Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Kare ya ta da gobara a gida
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus