A yau ne za a gurfanar da yan adawar siyasa guda 40 da ake tuhumarsu  da aikata laifukan dake barazana ga tsaron kasa, a shari’ar da ƙungiyoyin kare hakkin bil adama suke daukarta a matsayin bi ta da kullin siyasa.

Wadanda ake tuhumar sun hada da jami’an diflomasiyya da yan siyasa da lauyoyi da kuma yan jarida dake sukar salon mulkin shugaban kasar Kais Saied.

Zargin yi wa tsaron ƙasa zagon kasa da kuma shiga kungiyar yan ta’adda zai fuskanci hukunci mai tsananin, ciki har da hukuncin kisa.

Tun a shekara ta 2023 ne ake tsare da wasu , yayin da da dama kuma suka tsere zuwa kasashen ketare.

Masu fafutukar kare hakkin bil adama sun yi kira da a gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis don nuna adawa da shari’ar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila

Shugabannin kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombia sun jaddada aniyarsu ta hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila amfani da tashar jiragen ruwansu, a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi a zirin Gaza.

“Za mu hana jiragen ruwa da ke dauke da kayan aikin soji zuwa Isra’ila amfani da tashoshin jiragen ruwanmu; kamar yadda,” Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, Firayim Ministan Malaysia Anwar Ibrahim da Shugaban Colombia Gustavo Petro suka rubuta a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da mujallar harkokin waje ta buga a wannan makon.

Sun jaddada cewa yakin da Isra’ila ke yi a Gaza ya fallasa gazawar tsarin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen rashin hukunta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi.

Malesiya da Colombia na daga cikin kasashen da suka goyi bayan korafin kisan kiyashin da kasar Afrika ta kudu ta kai kan Isra’ila a kotun duniya ta ICJ.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Yamen Ta yi Alwashin Fadada Hare-hare Kan Israila Matukar Ta Dawo Da Kai Hari A Gaza.
  • Za A Sake Gurfanar da Blatter Da Platini Kan Zargin Cin Hanci
  • Miji ya yi yunƙurin kashe matarsa kan zargin maita
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD Ta Ce Sauye-Sauyen Da Ke Faruwa A Amurka Zai Shafi Al-Amura Da Dama A Majalisar
  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji A Gaza
  • MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza
  • Kwance Damarar Dakarun Hashdu Zai Ragewa Harkokin Tsaron Kasar Iraki Aminci
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila