Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya
Published: 4th, March 2025 GMT
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Shamsedeen Babatunde Ogunjimi a matsayin sabon Akanta Janar na Tarayya.
Naɗin nasa, wanda aka amince da shi a yau Talata, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.
Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace An horas da masu unguwannin Katsina kan sasanta jama’aAna iya tuna cewa, tun a watan Disambar da ya gabata ne aka bayyana Ogunjimi mai shekaru 57 a matsayin magajin Madehin.
Daga baya wani aka naɗa wani kwamitin ƙwararru da zai tantance wanda ya haɗa da manyan daraktocin daga a ma’aikatun gwamnatin tarayya daban-daban.
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar, ta ce kwamitin ya yi tantancewar bisa matakai uku masu tsauri da suka haɗa da a rubuce, gwajin ƙwarewar fasahar sadarwar da kuma hira ta baka.
Ogunjimi ya kammala karatunsa na digiri a Jami’ar Nijeriya, Nsukka, a shekarar 1990, inda ya sami digiri na farko a fannin lissafin kuɗi.
Ya kuma samu wani digiri na biyun a wannan fannin a Jami’ar Legas.
Kazalika, sabon Akanta Janar ɗin mamba ne a Cibiyar Akantoci na Nijeriya da Cibiyar Haraji ta Nijeriya.
Sanarwar ta ƙara da cewa, Shugaba Tinubu ya taya Ogunjimi murna, ya kuma buƙaci da ya hidimta wa Nijeriya bisa gaskiya, ƙwarewa, da sadaukarwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Akanta Janar
এছাড়াও পড়ুন:
Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar Nijeriya
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars wacce ake wa laƙabi da Masu Gida ta doke abokiyar karawarta Enugu Rangers da ci 2-1 a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.
Wasan wanda aka fara da karfe 4 na yammacin ranar Lahadi, ya na daga cikin manyan wasanni masu zafi da ke ɗaukar hankalin masu sha’awar ƙwallon ƙafa a Nijeriya.
Kano Pillars Ta Dakatar Da Kocinta Na Tsawon Makonni Uku Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?Rabiu Ali da Jerry Alex ne su ka jefa wa Pillars ƙwallayensu biyu a wasan, da wannan sakamakon Sai Masu Gida su ka koma matsayi na 4 akan teburin gasar Firimiyar Nijeriya.
Ƙungiyar ta Kano ta dakatar da kocinta Usman Abdallah, inda mataimakinsa Ahmed Garba Yaro Yaro ya jagorance ta a wasanni uku na baya bayan nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp