HausaTv:
2025-04-25@10:59:30 GMT

Masu Alaka

Published: 4th, March 2025 GMT

Iran Tayi Tir Da Shirin Shugaban Amurka Na Sake Tsugunar Da Al’ummar Gaza

Kakakin gwamnatin kasar iran Fatime mohajerani ta yi tir da aniyar  shugaban Amurka Donald trumph na kwashe alummar gaza zuwa wasu  wurare, kuma ta biyyana shi a matsayin ci gaba da siyasar kisan kare dangi kan alumma falasdinu,

Shugaban na Amurka Donald trump yayi wannan bayanin ne a taron manema  labarai  da yayi a fadar white hause da fira ministan isra’ila binjamin natanyaho a watan jiya, inda ya nuna aniyarsa ta kwashe alumma yankin gasa zuwa wasu kasashen larabawa.

Tare da gina wajen shakatawa da babbar tashar jiragen ruwa a wajen.

Shuwagabannin  kasashen laraba wa da na musulmi sun jadda mastayinsu na amincewa da yancin falasdinawa tare da yin watsi da duk wani yunkuri na rabasu da gidajensu.

Wasu masharhanta na ganin shirin na Amurka zai jawo a mata mayar da ita saniyar ware a harkokin diplomasiya har ma tsakaninta da sauran kawayenta a yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana farin cikisa bisa da shirye-shiryen da Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa NAHCON, ta gudanar ya zuwa yanzu, domin aikin Hajjin shekarar 2025.

Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ne ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin tattaunawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa, bayan da ya jagoranci membobin hukumar ta NAHCON domin gabatar wa Mataimakin Shugaban Ƙasa bayanai kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2025.

Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa ne ke sa ido kan ayyukan NAHCON, kuma Hukumar ta shaida wa Sanata Kashim Shettima cewa an kammala dukkan shirye-shiryen da suka wajaba domin fara aikin Hajjin 2025 da jigilar mahajjata zuwa ƙasar Saudiyya daga ranar 9 ga Mayu, 2025.

A nasa jawabin bayan ganawar, Kwamishinan NAHCON mai kula da ayyuka, Prince Anofi Elegushi ya bayyana cewa an riga an kammala shirye-shirye a Makka, Madina da sauran wurare domin gudanar da  aikin Hajji cikin sauki.

Ya ce, “Mun tanadi masaukai a Makka, da Madina da sauran wurare, an kuma shirya su domin tarɓar mahajjatanmu, inda muka  samu isassun gadajen, tare da biyan kuɗin abinci mai kyau kuma isasshe ga dukkan mahajjata. Mun zaɓi ranar 9 ga watan Mayu domin tashin jirgin farko zuwa Madina, muna kuma fatan kammala jigilar zuwa Saudiyya kafin ranar 24 ga watan Mayu, kuma mu fara dawo da mahajjata daga ranar 13 ga Yuni har zuwa 2 ga Yuli.”

A  jawabinsa tun da farko, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya bukaci Hukumar da ta tabbatar da cewa kowa yana bakin kokarinsa domin tabbatar da nasarar aikin Hajjin bana.

“Ya zama wajibi a dauki dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da nasarar aikin Hajjin 2025. Wannan nauyi ne a kanmu ga ‘yan Najeriya da mahajjata, domin mu tabbatar da aikin Hajji mai inganci.” In ji shi

 

Safiyah Abdulkadir

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka