Kasar Yamen Ta yi Alwashin Fadada Hare-hare Kan Israila Matukar Ta Dawo Da Kai Hari A Gaza.
Published: 4th, March 2025 GMT
Rahotanni sun nuna cewa kasar Yamen ta gargadi isra’ila game da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a gaza, kana ta yi alkawarin fadada hare-harenta a tel Avivi matukar ta dawo da kai hari kan alummar falasdinu,
Tace: matakin da isra’ila ta dauka na hana shigar da kayayyakin agaji da jin kai a yankin gaza, da kuma rufe dukkan mashigar dake isa zuwa yankin, take dukkan dokokin kasa da kasa ne da kuma yarjejeniyar da aka cimma.
Ana sa bangaren shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar yamen sayyid Abdul malik Hutsi ya bayyana cewa matukar Isra’ila ta dawo da kai hari a yankin Gaza to za ta mayar da martani mai tsananin a ko ina a Israila musamman birnin tel aviv.
Wannan sanarwar ta jawo damuwa sosai ga manyan jami’an tsaron Isra’ila , kuma sun dauki gargadin na Ansarullah da gaske domin zai jefa su cikin mawuyacin yanayi fiye da na baya a cewarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin Boko Haram Da ISWAP: An Kashe Masunta 18, Mutane Da Yawa Sun Bace
Ƴan ta’addan Boko Haram sun kashe masunta 18, a wani harin da suka kai a yankin Mobbar, wanda ke arewacin Jihar Borno, kusa da iyakar Jamhuriyar Nijar. Harin ya faru ne a kogin Fadana-Garuwa a yankin Duji, lokacin da mayakan suka kai hari cikin ruwan, inda suka zargi masu kamun kifin da haɗin kai da ‘yan ta’addan ISWAP.
A cewar wani mai kamun kifi da ya yi magana da wakilinmu, Boko Haram sun zo da yawan gaske suka yi ta kai hari kan masu kamun kifin, suna zargin su da kai rahoton maɓoyarsu ga ‘yan ta’addan ISWAP. Sun tattara su duka, suka kashe su, sannan suka yi barazanar cewa wannan hukunci ne ga wanda ke aiki tare da ISWAP.
Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan YobeAn tabbatar da cewa yankin na cikin ikon Boko Haram da sauran ruwan da ke kusa da iyakar Nijar, kuma wannan hari yana da alaƙa da rikicin dake tsakanin bangarorin Boko Haram da ISWAP. An samu gawarwakin mutanen 18, yayin da wasu da dama suka bace. Tuni al’ummar yankin suka gudanar da jana’izar su bisa tsarin Musulunci.
A cikin watannin da suka gabata, duka ɓangarorin Boko Haram da ISWAP sun ƙara yawan hare-haren su kan fararen hula da sansanin Soja a jihohin Borno, Yobe, da Adamawa, wanda ya haifar da ƙarin tashe-tashen hankula a yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp