Kasar Yamen Ta yi Alwashin Fadada Hare-hare Kan Israila Matukar Ta Dawo Da Kai Hari A Gaza.
Published: 4th, March 2025 GMT
Rahotanni sun nuna cewa kasar Yamen ta gargadi isra’ila game da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a gaza, kana ta yi alkawarin fadada hare-harenta a tel Avivi matukar ta dawo da kai hari kan alummar falasdinu,
Tace: matakin da isra’ila ta dauka na hana shigar da kayayyakin agaji da jin kai a yankin gaza, da kuma rufe dukkan mashigar dake isa zuwa yankin, take dukkan dokokin kasa da kasa ne da kuma yarjejeniyar da aka cimma.
Ana sa bangaren shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar yamen sayyid Abdul malik Hutsi ya bayyana cewa matukar Isra’ila ta dawo da kai hari a yankin Gaza to za ta mayar da martani mai tsananin a ko ina a Israila musamman birnin tel aviv.
Wannan sanarwar ta jawo damuwa sosai ga manyan jami’an tsaron Isra’ila , kuma sun dauki gargadin na Ansarullah da gaske domin zai jefa su cikin mawuyacin yanayi fiye da na baya a cewarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za’a Gurfanar Da Mutane 40 A Gaban Kotu Kan Zargin Yin Barazana Ga Tsaron Kasa A Tunisiya.
A yau ne za a gurfanar da yan adawar siyasa guda 40 da ake tuhumarsu da aikata laifukan dake barazana ga tsaron kasa, a shari’ar da ƙungiyoyin kare hakkin bil adama suke daukarta a matsayin bi ta da kullin siyasa.
Wadanda ake tuhumar sun hada da jami’an diflomasiyya da yan siyasa da lauyoyi da kuma yan jarida dake sukar salon mulkin shugaban kasar Kais Saied.
Zargin yi wa tsaron ƙasa zagon kasa da kuma shiga kungiyar yan ta’adda zai fuskanci hukunci mai tsananin, ciki har da hukuncin kisa.
Tun a shekara ta 2023 ne ake tsare da wasu , yayin da da dama kuma suka tsere zuwa kasashen ketare.
Masu fafutukar kare hakkin bil adama sun yi kira da a gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis don nuna adawa da shari’ar.