A ko da yaushe kasar Sin na tsayawa tare da kasashe masu tasowa a matsayinta na kasa mai tasowa kuma mamba na wadannan kasashe.

Kakakin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, Lou Qinjian ne ya bayyana hakan a ranar Talata a taron manema labarai, inda ya ce, kasar Sin za ta rika shiga a dama da ita, kuma za ta kasance mai bayar da shawarwari kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa.

Da yake tsokaci game da matakin da Amurka ta dauka na sanya karin harajin kashi 10 cikin 100 kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, Lou ya ce, daukar matakin da Amurka ta yi bisa radin kai ya saba wa ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya, kuma ya kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar masana’antu da tsarin samar da kayayyaki a duniya. Kakakin ya kara da cewa, kamata ya yi Amurka ta yi aiki tare da kasar Sin kuma su fahimci juna don warware takaddamar cinikayya ta hanyar yin shawarwari bisa daidaici.

Ya kuma kara da cewa, kasar Sin tana matukar martaba dangantakarta da kasashen Turai, kuma sassan biyu abokan hulda ne dake ba da gudummawa ga samun nasarar juna. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya

Kungiyar da take wakiltar Iran a wasannin Taekwondo na duniya a kasar Sin, ta sami lambobin yabo 8 a ranar farko da bude gasar ta kasa da kasa.

An  fara wasannin na Tikondu a garin Tayan dake kasar China wanda shi ne karo na 7 da kuma ‘yan wasa 491 daga duniya suke gasa.

Daga cikin lambobin yabon din da tawagar ta Iran ta lashe da akwai gwala-gwalai 4, azurfa 3 da kuma tagulla.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Xi: Yake-yaken Haraji Da Kasuwanci Na Tauye Hakkoki Da Muradun Dukkan Kasashe
  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka