Aminiya:
2025-03-04@20:44:43 GMT

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja

Published: 4th, March 2025 GMT

Ana fargabar cewa wasu masu ta’adar garkuwa da mutane sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), David Shikfu Parradang a Abuja.

Majiyoyi sun shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya Zagazola Makama cewa ’yan ta’addan sun ɗauke Parradang a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar da safiyar wannan Talatar.

Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace

Makama ya ce ’yan ta’addan sun biyo sawun tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ne bayan ya ciro kuɗi a banki, inda suka karɓe kuɗin sannan kuma suka kashe shi.

Wannan lamari dai ya sake ɗaga hankalin mazauna Abuja a fannin tsaro musamman yadda a bayan nan ta’adar kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ƙara ƙamari.

Parradang dai ya shafe fiye da shekaru 30 yana aiki a Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, inda ya riƙe muƙamai daban-daban a faɗin ƙasar cikin har da kujerar Kwanturola-Janar na ƙasa.

Ya yi aiki a jihohin Kano, Legas, Kwara, Enugu da Abuja, sannan ya yi kwasa-kwasai na neman ƙwarewa da sanin makamar aiki a nan cikin gida da ƙetare.

Tuni hukumomin tsaro suka soma gudanar da bincike domin bankaɗo masu hannu a wannan aika-aikar.

Kawo yanzu babu wata sanarwa da hedikwatar Hukumar Shige da Ficen ta fitar dangane da faruwar lamarin.

Sai dai wani jami’anta a hedikwatar da ke Abuja ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa a jira hukumar ta fitar da sanarwa a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Shikfu Parradang garkuwa da mutane Hukumar Shige da Fice Hukumar Shige da

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade a Ƙaramar Hukumar Arewa, Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum shida a makon da ya gabata.

Maharan sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, sannan suka hallaka ɗaya a Bagiza yayin harin da suka kai domin satar shanu.

Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali

Wannan ta’addanci ya jefa mazauna yankin cikin tsananin fargaba.

Gwamna Nasir Idris ya bayar da tabbacin inganta a tsaro jihar.

Ganin yadda mutane ke cikin tsoro, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kai ziyarar jaje ƙauyukan a ranar Asabar.

Ya tabbatarwa da al’ummar yankin cewa gwamnati na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar tsaro, musamman a yankin Kebbi ta Kudu.

Gwamnan ya bayyana cewa mafi yawan hare-haren da ake fuskanta a Kebbi na zuwa ne daga maƙwabtan jihohi.

“Tun daga lokacin da muka hau mulki, muna ɗaukar matakan da suka dace domin magance matsalar tsaro, kuma muna samun ci gaba.

“Rashin ɗaukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro a wasu maƙwabtan jihohi yana bai wa ’yan bindiga damar kutsowa cikin yankunanmu suna kai hari,” in ji Gwamnan.

Ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

A yayin ziyarar, Gwamna Nasir Idris ya bayar da tallafin miliyan 10 ga iyalan waɗanda aka kashe.

Haka kuma, ya bayar da umarnin gina Masallacin Juma’a da kuma bohol guda biyu da ke amfani da hasken rana a ƙauyen Rausa Kade.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Hon. Sani Aliyu Tela, ya jinjina wa Gwamnan bisa wannan kulawa.

Ya bayyana cewa harin ya faru ne a daren Alhamis, inda ’yan bindiga suka kai farmaki domin satar dabbobi.

“Sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, suka harbi mutum ɗaya a Bagiza. Mun yaba da kulawar da kake ba mu,” in ji shi.

Jama’a dai na fatan matakan da gwamnati ke ɗauka za su kawo ƙarshen hare-haren da suka addabi yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Fashi Da Makami Sun Kashe Tsohon Babban Kwanturolan Hukumar NIS A Abuja 
  • ‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’
  • A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya — ’Yan sanda
  • RAMADAN: Gwamnatin Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar 
  • HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Gargadi Malaman Da Ba Sa Zuwa Aiki
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus