Aminiya:
2025-04-25@11:01:57 GMT

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja

Published: 4th, March 2025 GMT

Ana fargabar cewa wasu masu ta’adar garkuwa da mutane sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), David Shikfu Parradang a Abuja.

Majiyoyi sun shaida wa ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya Zagazola Makama cewa ’yan ta’addan sun ɗauke Parradang a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar da safiyar wannan Talatar.

Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace

Makama ya ce ’yan ta’addan sun biyo sawun tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ne bayan ya ciro kuɗi a banki, inda suka karɓe kuɗin sannan kuma suka kashe shi.

Wannan lamari dai ya sake ɗaga hankalin mazauna Abuja a fannin tsaro musamman yadda a bayan nan ta’adar kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ƙara ƙamari.

Parradang dai ya shafe fiye da shekaru 30 yana aiki a Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, inda ya riƙe muƙamai daban-daban a faɗin ƙasar cikin har da kujerar Kwanturola-Janar na ƙasa.

Ya yi aiki a jihohin Kano, Legas, Kwara, Enugu da Abuja, sannan ya yi kwasa-kwasai na neman ƙwarewa da sanin makamar aiki a nan cikin gida da ƙetare.

Tuni hukumomin tsaro suka soma gudanar da bincike domin bankaɗo masu hannu a wannan aika-aikar.

Kawo yanzu babu wata sanarwa da hedikwatar Hukumar Shige da Ficen ta fitar dangane da faruwar lamarin.

Sai dai wani jami’anta a hedikwatar da ke Abuja ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa a jira hukumar ta fitar da sanarwa a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Shikfu Parradang garkuwa da mutane Hukumar Shige da Fice Hukumar Shige da

এছাড়াও পড়ুন:

2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba

Kujeru dubu daya da dari hudu da bakwai ne aka ware wa hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Taraba domin maniyyata bana.

 

Babban Sakataren Hukumar mai barin gado Umar Ahmed Chiroma ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan matakin da ake na shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana na 2025 ba tare da tangarda ba.

 

Aikin Hajji daya ne daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar kuma Musulmin muminai na gudanar da aikin Hajji a kowace shekara akalla sau daya a rayuwarsu.

 

Chiroma ya ce hukumar ta kai wani mataki na ci gaba ta fannin shirye-shirye kamar yadda hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta bayar, inda ya ce sama da maniyyatan jihar 500 ne suka kammala biyan kudadensu.

 

Alhaji Ahmed Umar Chiroma ya kara da cewa a halin yanzu sama da Alhazai dubu biyar ne suka biya kudin aikin Hajji, yana mai kira ga sauran maniyyatan da su gaggauta biya domin cika wa’adin da hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kebe.

 

Ya yi bayanin cewa hukumar ta samu karancin masu zuwa aikin hajjin ba, inda ya danganta hakan ga tabarbarewar tattalin arziki ganin yadda amfanin gona da shanu suka ragu matuka a farashi.

 

Sakataren zartarwa ya bayyana manoma da makiyaya a matsayin manyan masu biyan kujerun aikin Hajji a jihar, inda ya nuna cewa gwamnatin jihar ta biya kujeru hamsin (50).

 

Chiroma ya ci gaba da bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara yin alluran rigakafi da tantance maniyyatan da ke shirin kammala shirye-shiryen aikin Hajji.

 

A cewarsa, hukumar ta kammala shirye-shirye a sansanin Alhazai a Jalingo, babban birnin jihar.

 

Sakataren zartarwa mai barin gado ya bayyana karara cewa jami’an hukumar sun ziyarci kasar Saudiyya inda suka samu masaukin da suka dace da mahajjatan jihar Taraba.

 

Umar Ahmed Chiroma ya yabawa Gwamna Agbu Kefas bisa daukar nauyin Alhazai hamsin, yana mai jaddada cewa wannan karimcin zai taimaka matuka wajen taimakawa mutane da dama wajen gudanar da aikin hajjin 2025.

 

 

Sani Sulaiman

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • Kotu A Kano Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Matashi Da Ya Kashe Ƙanwarsa Da Kishiyar Mahaifiyarsa
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano