Leadership News Hausa:
2025-04-24@18:17:54 GMT

Dorawa Wasu Laifi Ba Zai Kawo Ci Gaban Da Amurka Ke Muradi Ba

Published: 5th, March 2025 GMT

Dorawa Wasu Laifi Ba Zai Kawo Ci Gaban Da Amurka Ke Muradi Ba

A yau Talata, kasar Sin ta bakin ma’aikatar kula da harkokin kasuwanci ta kasar ta bayyana rashin jin dadinta game da karin harajin da Amurka ta yi ikirarin sanyawa kayayyakin kasar, bisa kafa hujja da maganin Fentanyl.

Kamar yadda kakakin ma’aikatar ya bayyana, Sin tana daya daga cikin kasashe mafiya tsauraran matakan yaki da miyagun kwayoyi ko sarrafa su.

Tabbas kasar Sin kasa ce mai sa ido da daukar tsauraran matakan dakilewa da yaki da tu’ammali da duk wani abu mai illa, musammam miyagun kwayoyi, kuma tana iyakar kokarinta kan wannan batu. Idan ba a manta ba, kasar Sin ce ta jagoranci duniya wajen tsara jerin rukunin kwayoyin Fentanyl da sauran abubuwan da suka jibance shi a watan Mayun 2019, inda ta taka muhimmiyar rawa wajen hana samarwa da safara da kuma amfani da shi. Baya ga haka, tana iyakar kokarinta wajen hada gwiwa da taimakawa Amurka don shawo kan batun.

Kakaki: A Ko Da Yaushe Kasar Sin Tana Tsayawa Tare Da Kasashe Masu Tasowa Za A Sake Gurfanar da Blatter Da Platini Kan Zargin Cin Hanci

Sai dai, duk da wannan kokari da Sin take yi, har yanzu Amurka na kafa hujja da batun wajen kakaba takunkumin ba gaira ba dalili da kuma kakaba haraji duk da cewa, kasashen biyu sun yi tattaunawa mai zurfi tare da hada hannu kan batun dakile tu’ammali da Fentanyl, kuma an samu kyawawan sakamako.

Akwai bukatar Amurka ta gane cewa, rikici da fito na fito ba zai taba kawo ci gaban da take nema ba. Haka kuma, yakin haraji da cinikayya, tsaiko zai kawo tare da mayar da hannun agogo baya don gane da nasarori da sakamakon da aka samu wajen dakile Fentanyl din da ma dangantakar dake tsakaninta da Sin. Bugu da kari, ya kamata Amurka ta rika kokarin lalubo inda take da matsaloli ta kuma gyara su, maimakon har kullum ta kasance mai dorawa wasu laifi. Kaucewa daukar nauyin matsalolinta da shawo kan su, ba zai taba kawo mata mafita ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: China da Rasha abokan hulda ne na tushe ga Iran bisa kyakkyawan tsari

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana kasashen China da Rasha a matsayin abokan huldar na tsari a kan tubalin manyan tsare-tsare ga Iran, kuma ya dace kasashen uku su ci gaba da tuntubar juna a fannoni daban daban.

A yayin da ya isa birnin Beijing, yayin da yake amsa tambaya game da makasudin ziyararsa a kasar China a jajibirin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, Araqchi ya bayyana cewa: Kasashen China da Rasha abokan hulda ne na kut-da-kut da Iran. Sun kasance tare da Iran a lokutan wahala, kuma abu ne mai kyau cewa Iran suna ci gaba da tuntubar juna tare da su a fagage daban-daban, musamman a yanzu da aka tabo batun tattaunawa da Amurka a fakaice.

Araqchi ya ci gaba da cewa: “Suna bukatar su sanar da abokansu da ke kasar China cikakkun bayanai game da abubuwan da ke faruwa tare da tuntubarsu, kuma sun yi hakan a makon da ya gabata a kasar Rasha.” Inda ahalin yanzu suke kasar China, kuma zai isar da sakon shugaba kasar Iran Mas’ud Pezeshkian, kuma idan Allah ya yarda za su yi tattaunawa mai kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China
  • Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa