Dorawa Wasu Laifi Ba Zai Kawo Ci Gaban Da Amurka Ke Muradi Ba
Published: 5th, March 2025 GMT
A yau Talata, kasar Sin ta bakin ma’aikatar kula da harkokin kasuwanci ta kasar ta bayyana rashin jin dadinta game da karin harajin da Amurka ta yi ikirarin sanyawa kayayyakin kasar, bisa kafa hujja da maganin Fentanyl.
Kamar yadda kakakin ma’aikatar ya bayyana, Sin tana daya daga cikin kasashe mafiya tsauraran matakan yaki da miyagun kwayoyi ko sarrafa su.
Sai dai, duk da wannan kokari da Sin take yi, har yanzu Amurka na kafa hujja da batun wajen kakaba takunkumin ba gaira ba dalili da kuma kakaba haraji duk da cewa, kasashen biyu sun yi tattaunawa mai zurfi tare da hada hannu kan batun dakile tu’ammali da Fentanyl, kuma an samu kyawawan sakamako.
Akwai bukatar Amurka ta gane cewa, rikici da fito na fito ba zai taba kawo ci gaban da take nema ba. Haka kuma, yakin haraji da cinikayya, tsaiko zai kawo tare da mayar da hannun agogo baya don gane da nasarori da sakamakon da aka samu wajen dakile Fentanyl din da ma dangantakar dake tsakaninta da Sin. Bugu da kari, ya kamata Amurka ta rika kokarin lalubo inda take da matsaloli ta kuma gyara su, maimakon har kullum ta kasance mai dorawa wasu laifi. Kaucewa daukar nauyin matsalolinta da shawo kan su, ba zai taba kawo mata mafita ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaei ya yi kira ga gwamnatin kasar Turkiya ta sake tunani kan kalamanta dangane da JMI.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei ya na fadar haka a jiya Litinin, a taron mako mako da ya saba gabatarwa a ko wace litinin. Ya yi wannan kiran ne bayan wata maganan da ministan harkokin wajen kasar Turkiyya Hakan Fidan ya yi dangane da kasar Iran.
Labarin ya kara da cewa, Hakan Fiddan ya bayyana cewa shirye-shiryen JMI a kasar Siriya masu rusa kasar ne, kafin juyin mulkin da Turkiyan ta dauki nauyinsa a baya-bayan nan a kasar Siriya.
Ya ce: Fidan yana magana kan gagarumin taron Jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasaralla wanda aka gudanar a birnin Beirut na kasar Lebanon a ranar Lahadi 23 ga watan Fabrairun da ta gabata. Tare da halattar manya-manyan jami’an gwamnatin kasar.
Baghaei ya ce: Ministan yana nufin ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya kai zuwa taron na Jana’iza da ganawar da yayi da Jami’an gwamnatin kasar Lebanon a lokacin, da zuwan sa Geneva inda ya halarci taron kwance damarar makaman Nukliya, da kuma ganawarsa da ministocin harkokin wajen kasashen Indonasia, Bahrain, Kuwait da kuma wasu a gefen taron.
Ya ce Iran tana maganar a dai dogaro da manya-manyan kasashen duniya, kuma kasashen yankin su magance matsalolinsu da kansu.