Har Kullum Jama’ar Kasar Sin Suna Adawa Da Nuna Fin Karfi
Published: 5th, March 2025 GMT
A yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda a yayin taron, wani dan jarida ya gabatar da tambaya game da matakin Amurka, na sake kakabawa Sin karin harajin kashi 10 cikin dari, bisa fakewa da batun sinadarin kashe radadi na Fentanyl.
Ya ce, har kullum jama’ar kasar Sin suna adawa da nuna fin karfi, da yin matsin lamba, da tilastawa, da kuma barazana, saboda hakan ba hanya ce da ta dace a bi yayin mu’ammala da kasar Sin ba.
Ya kara da cewa, idan bangaren Amurka yana son warware batun Fentanly, ya kamata ya tattauna tare da bangaren Sin bisa daidaito, da mutunta juna, da samun moriyar juna, har a kai ga warware matsalolin dake tsakani. To amma idan har Amurka na da wasu manufofi, kuma ta nace a kan kaddamar da yakin haraji, da yakin kasuwanci ko wani yaki na daban, kasar Sin za ta tunkari yakin har zuwa karshe.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba
Kakakin rundunar tsaron teku ta kasar Sin Liu Dejun, ya bayyana a yau Lahadi cewa, an kori wani jirgin kamun kifi na kasar Japan da ya shiga yankin ruwan kasar Sin na tsibirin Diaoyu Dao ba bisa ka’ida ba.
A cewarsa, rundunar ta dauki matakan da suka dace bisa doka, ta gargadi jirgin sannan ta kore shi, bayan ya shiga yankin ruwan kasar Sin tsakanin ranar Asabar da Lahadi.
Sau Biyu Ake Yin Girbin Aya A Shekara – RMRDC Gwamnatin Yobe Ta Ƙaryata Rahoton Bayyanar Boko Haram A Babban Birnin JiharDa yake bayyana tsibirin na Diaoyu Dao da tsibiran dake karkashinsa a matsayin mallakin kasar Sin, Liu Dejun ya bukaci Japan ta gaggauta dakatar da ayyukanta da suka saba doka a wadannan yankuna.
Har ila yau, rundunar ta ce, za ta ci gaba da ayyukanta na tabbatar da doka a yankin ruwa na tsibirin Diaoyu Dao da kare yankuna da hakkoki da muradun kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp