Har Kullum Jama’ar Kasar Sin Suna Adawa Da Nuna Fin Karfi
Published: 5th, March 2025 GMT
A yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda a yayin taron, wani dan jarida ya gabatar da tambaya game da matakin Amurka, na sake kakabawa Sin karin harajin kashi 10 cikin dari, bisa fakewa da batun sinadarin kashe radadi na Fentanyl.
Ya ce, har kullum jama’ar kasar Sin suna adawa da nuna fin karfi, da yin matsin lamba, da tilastawa, da kuma barazana, saboda hakan ba hanya ce da ta dace a bi yayin mu’ammala da kasar Sin ba.
Ya kara da cewa, idan bangaren Amurka yana son warware batun Fentanly, ya kamata ya tattauna tare da bangaren Sin bisa daidaito, da mutunta juna, da samun moriyar juna, har a kai ga warware matsalolin dake tsakani. To amma idan har Amurka na da wasu manufofi, kuma ta nace a kan kaddamar da yakin haraji, da yakin kasuwanci ko wani yaki na daban, kasar Sin za ta tunkari yakin har zuwa karshe.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin cewa, babu wata tattaunawa da aka yi ta wayar tarho tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka a baya-baya nan, haka kuma bangarorin biyu ba su cimma wata yarjejeniya ko su tuntubi juna game da batun haraji ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp