Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-gilu
Published: 5th, March 2025 GMT
Wasa ya koma kuka bayan da wani mai wasan barkwanci manne laɓɓansa ba sa buɗewa bayan da ya shafa musu gam din sufa-gilu a yayin da yake yin bidiyo kai-tsaye domin ƙayatar da masu bibiyarsa.
Mutumin ya shafa gilu ne, inda ya manne laɓɓansa, wanda cikin dakika kaɗan, mannewar ta kama fatar laɓɓan kamar yadda ya so, inda hakan ya sa yabar laɓɓansa a rufe sosai.
A zamanin da ake amfani da shafukan sada zumunta na zamani, mutane sukan yi iyakacin ƙoƙarinsu don samun mabiya da sakonsu zai kai gare su a intanet.
Raye-rayen zuwa abubuwan barkwanci, suna yin tasiri a shafukan sada zumunci na zamani.
Kwanan nan, wani bidiyo na wani mutum ɗan kasar Philippines ya ɗauki hankalin jama’a a intanet.
A cikin bidiyon, mutumin ya shafa sufa-gilu a laɓɓansa a matsayin wani ɓangaren na wasan barkwanci, amma lamarin ya sauya zuwa wani abun daban.
Bidiyon da tashar Talabijin ta Badis TV ta yada a shafin Insitagaram ya nuna wani mutumi zaune a cikin shago, rike da robar sufagilu kuma cikin wasa yana nuna kansa a kyamara.
Yana shafa shi, yana mannewa a lebbansa, amma cikin dakika kadan, mannewa ta kama fatun laɓɓansa yadda yake so, hakan dole ya sa ya bar laɓɓan a rufe sosai.
Da farko, mutumin ya bayyana yin hakan a matsayin nishadantarwa, yana dariya kamar ya yi nasara. Sai dai dariyarsa ta koma kuka, inda ya yi ta ƙoƙarin buɗe baki.
Nishadantarwarsa ta rikide zuwa firgici lokacin da ya gane laɓɓansa ba za su rabu ba, duk ya yi kokarin yin hakan.
Bayan wani lokaci sai hawaye hawaye suka fara gangarowa a fuskarsa yayin da yanayin ya yi tsanani, wanda hakan ya sa shi cikin damuwa.
Bidiyon ya sami ra’ayoyi sama da miliyan 6.7 na mabiya shafin kuma ya haifar da martani da yawa daga masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani.
Da yake mayar da martani ga bidiyon, wani mabiyin shafin ya yi dariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barkwanci
এছাড়াও পড়ুন:
Masu Alaka
Iran Tayi Tir Da Shirin Shugaban Amurka Na Sake Tsugunar Da Al’ummar Gaza
Kakakin gwamnatin kasar iran Fatime mohajerani ta yi tir da aniyar shugaban Amurka Donald trumph na kwashe alummar gaza zuwa wasu wurare, kuma ta biyyana shi a matsayin ci gaba da siyasar kisan kare dangi kan alumma falasdinu,
Shugaban na Amurka Donald trump yayi wannan bayanin ne a taron manema labarai da yayi a fadar white hause da fira ministan isra’ila binjamin natanyaho a watan jiya, inda ya nuna aniyarsa ta kwashe alumma yankin gasa zuwa wasu kasashen larabawa. Tare da gina wajen shakatawa da babbar tashar jiragen ruwa a wajen.
Shuwagabannin kasashen laraba wa da na musulmi sun jadda mastayinsu na amincewa da yancin falasdinawa tare da yin watsi da duk wani yunkuri na rabasu da gidajensu.
Wasu masharhanta na ganin shirin na Amurka zai jawo a mata mayar da ita saniyar ware a harkokin diplomasiya har ma tsakaninta da sauran kawayenta a yankin.