HausaTv:
2025-04-25@16:57:31 GMT

Jagoran Juyin Musulunci Ya Bayar Da Tallafin Kudi Domin Sakin Fursunoni

Published: 5th, March 2025 GMT

Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayar da tallafin kudin da sun kai Riyal biliyan 40 ga kungiyoyin agaji da suke aiki domin ganin an saki frusunonin da su ka aikata laifuka ba cikin ganganci ba.

 A kowace shekara  a cikin watan Ramadan mai alfarma kungiyoyin na agaji suna kaddamar da neman taimako saboda sakin fursunonin da su ka aikata laifuka ba a cikin ganganci ba.

Ana amfani da kudaden ne wajen biyar  fansa da diyya ga wadanda fursunonin su ka yi wa illa. Biyan fansa din dai ana yinsa ne  maimakon zartar da hukunci na Kisasi.

Watan azumin Ramadana da shi ne na 9 a  cikin kalandar musulunci yana da matsayin na musamman da ake son aikata alheri fiye da kowane lokaci a cikinsa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi

Gwamnatin Shugaban kasa John Mahama ta tsige Gertrude Torkornoo daga mukaminta na babbar mai shari’ar kasar, bisa wasu zarge-zarge da ake yi mata, domin bayar da damar gudanar da bincike.

Matakin da gwamnatin ta dauka na tsige babbar mai shari’ar ya jawo cece-kuce a tsakanin mutanen kasar.

Tsohon mai shigar da kara na kasar Godfrred Yeboah Dame ya yi tir da matakin na gwamnati da ya siffata da farmaki mafi girma akan ma’aikatar shari’a a tarihin kasar.”

 Ita kuwa jam’iyyar hamayya ta zargi shugaban kasa da tsoma baki a harkokin shari’ar kasar, domin nada alkalan da za su  zama masu biyayya ga jam’iyyar da take Mulki ta ( NDC).

Torkornoo da ta hau mukamin nata a 2023, kuma  ta kasance mace ta uku  da ta rike wannan mukamin a tsawon tarihin ma’aikatar shari’ar kasar. Har ya zuwa yanzu dai ba ta ce komai ba akan tuhume-tuhumen da ake yi ma ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Tuƙin Ganganci: Direba Ya Kashe Jami’in KAROTA
  • Jagora: Tafarkin Imaman Ahlul Bayti ( A.S) Na Gwgawarmaya Ne Da Jajurcewa
  • Gwamnatin Siriya Tana Daukan Matakan Matsin Lamba Kan Gwagwarmaya Domin Samun Yardan ‘Yan Sahayoniyya
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • Burkina Faso ta sanar da dakile wani yunkurin juyin mulkin a kasar
  • An daƙile yunƙurin juyin mulki a Burkina Faso