HausaTv:
2025-03-06@03:21:03 GMT

Kremlin: Putin Ya Amince Da Shiga Tsakanin Iran Da Amurka

Published: 5th, March 2025 GMT

Kafafen watsa labarun Rasha sun nakalto a jiya Talata cewa, shugaba Vladmir Putin ya amince da zama mai shiga tsakanin Iran da Amurka.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya amanci cewa, kafafen watsa labarun Rasha sun nakalto majiyar fadar mulkin kasar “Kremlin” na cewa shugaba Vladmir Putin zai zama mai shiga tsakanin Iran din da Amurka.

Haka nan kuma kafafen watsa labarun na Rasha sun ce; Rasha da Amurka sun amince su yi wata tattaunawa ta daban akan Iran”.

Mataimakin shugaban kasar Rasha ya ambaci cewa, a yayin zaman da kasashen biyu su ka yi a Riyadh na Saudiyya, sun tattauna akan abinda yake da alaka da Iran.

Majiyar ta kuma ce abinda kasashen biyu suke son yin Magana akansa shi ne, shirin makamashin Nukiliya na Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Zai Watsa Bikin Bude Zama Na Uku Na Majalisar CPPCC Karo Na 14

Kamfanin gungun gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG, zai watsa bikin bude zama na 3 na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin, wato CPPCC karo na 14 a gobe Talata 4 ga watan nan.

Za a bude taron ne da karfe 3 na rana bisa agogon Beijing. Kuma shugaban majalisar ta CPPCC Wang Huning, zai mika rahoton aikin zaunannen kwamitin koli na majalissar CPPCC.

Kazalika a yayin zaman, kafofin rediyo da na talabijin daban daban dake karkashin CMG, za su gudanar da shirye-shirye kai tsaye, kana su ma sabbin kafofin sadarwa na zamani za su shiga a dama da su a wannan aiki. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata
  • Taron Kasashen Turai Don Goyon Baya Ga Kasar Ukraine, Ya Watse Ba Tare Da Tsaida Irin Taimakon Da Zasu Yi Mata Ba
  • Masar: An Kawo Karshen Taron Kasashen Larabawa Na Musamman Akan Gaza
  • Gwamnatin Libya Ta Kore Cewa Za Ta Karbi Bakuncin Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira
  • Kasar Rasha ta ce Janye tallafin Soji da Amurka take bawa Ukrain zai kawo zaman lafiya.
  • Ba Za Mu Tattauna da Rasha Ba Sai Ta Daina Kai Mana Hari – Zelensky
  • Iran Ta Bukaci Turkiya Ta Kara Tunani Kan Kalamanta Dangane Da Iran
  • Angola Zata Shiga Shirin ‘Yankunan Kasuwanci’ Na Kungiyar SADC
  • CMG Zai Watsa Bikin Bude Zama Na Uku Na Majalisar CPPCC Karo Na 14