Babban magatakardar MDD Antonio Guterres  wanda ya halarci taron da kasashen larabawa suke yi a Masar, ya bayyana goyon bayansa ga tsarin da su ka bijiro da shi na sake gina yankin Gaza, ba tare da an fitar da Falasdinawa daga cikinsa ba.

Gutress ya ce; Ina maraba da kuma nuna cikakken goyon bayana ga shirin da taron kungiyar kasashen larabawa ta bijiro da shi na sake gina Gaza.

Gutrress ya kuma ce: MDD a shirye take ta shiga da karfi a yi wannan aikin da ita.

Haka nan kuma babban magatakardar MDD ya yi kira da a dauki duk matakin da ya kamata domin ganin ba a sake komawa yaki a Gaza ba.

Gutteres ya kuma ce, Gaza ba ta da makoma wacce ta wuce ta kasance a karkashin daular Falasdinawa.

Babban magatakardar MDD ya bayyana taron na kasashen larabawa da cewa yana da matukar muhimmanci domin daukar nauyi a jumlace da zai kai ga kawo karshen yakin Gaza.

A jiya Talata ne dai kasashen larabawa su ka hadu a Alkahira ta kasar Masar domin halartar taron tattauna hanyoyin sake gina Gaza da kuma kalubalantar manufar Amurka da HKI na korar Falasdinawa daga Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta

Munanan azabtarwa kan fursunonin Falasdinawa a gidajen kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila da suka hada da fyade da dangogin azaba

Rahoton da Hukumar Kula da Fursunoni Falasdinawa dakungiyar Fursunonin Falasdinawa da aka saka daga gidan kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila sun fiyar da rahoton hadin gwiwa a yau Alhamis, 24 ga watan Afrilun shekara ta 2025, da ya kunshi munanan shaida daga fursunonin Zirin Gaza da ke tsare a gidan yarin Negev da sansanin Ofer na gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila.

Rahoton ya bayyana yadda ake ci gaba da yin fyade da cin zarafi ga wadanda ake tsare da su a Gaza.

Wanda ake tsare da shi a sansanin Ofer ya bayyana cewa da gangan masu gadin sansanin suke kara radadin yadda wanda ake tsare da su da hakan ke kara masifar azabtarwar da ake gana musu. Haka kuma wanda ake tsare ana yi masa fyade a gaban ’yan uwansa da ake tsare da su, da nufin wulakanta shi da kuma rusa tunaninsa, da hakan ke kara tsoro da firgici a tsakanin sauran wadanda ake tsare da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Aniyar Kasarsa Ta Goyon Bayan Kudurorin Kyautata Yanayi Da Ci Gaba Marar Gurbata Muhalli
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • Dalilin Da Zai Iya Hana Ni Sake Bugawa Manchester United Wasa – Rashford
  • Kotu A Kano Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Matashi Da Ya Kashe Ƙanwarsa Da Kishiyar Mahaifiyarsa
  • Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno 
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya