Leadership News Hausa:
2025-04-25@06:09:58 GMT

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin

Published: 5th, March 2025 GMT

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin

A cewar rahoton, za a samar tare da aiwatar da wani tsari mai wa’adin shekaru 3, wanda zai mayar da hankali wajen karfafa bangaren ilimi.

Haka kuma, kasar za ta inganta raya ilimin dole mai inganci kuma bisa daidaito, tare da kara bayar da damar shiga makarantun sakandare.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, kasar Sin za ta inganta hada ilimin sana’o’i da ilimi na gama gari, tare da hada hannu da masana’antu da makarantu ta yadda ilimin sana’o’i zai kara dacewa da tsarin ilimi.

Rahoton ya kara da cewa, kasar Sin za ta aiwatar da gyare-gyare a makarantun gaba da sakandare cikin rukunoni, tare da daukar matakai masu kwari wajen fadada ingancin karatu da gaggauta samar da jami’o’i da bangarorin kwarewa da za su kai matsayi mafi kyau a duniya.

Kasar Sin ta ce, tana adawa da duk wani nau’i na kariyar cinikayya da zartar da ra’ayi na kashin kai, kuma za ta daukaka tabbatar da adalci da daidaito a duniya.

Rahoton ya kara da cewa, kasar za ta ci gaba da nacewa ga manufar diplomasiyya mai zaman kanta da bin tafarkin neman ci gaba cikin lumana.

A cewar rahoton, a shirye kasar Sin take ta hada hannu da sauran kasashen duniya wajen samar da duniya mai adalci da rabuwar iko tsakanin kasa da kasa da dunkule tattalin arzikin duniya, ta yadda kowa zai amfana da ita da inganta aiwatar da shawarar ci gaban duniya da ta samar da tsaro a duniya da ta wayewar kan al’ummun duniya. Haka kuma, za ta shiga a dama da ita wajen aiwatar da gyare-gyare a tsarin tafiyar da harkokin duniya da yayata shawarar gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil Adama da kuma samar da makomar zaman lafiya da ci gaba ga duniya.

Bugu da kari, rahoton ya ce, Sin za ta daukaka burinta na ganin dunkulewar kasar, inda ya ce, za ta inganta cibiyoyi da manufofin raya tattalin arziki da musayar al’adu da hadin kai a fadin mashigin Taiwan da fadada ayyukan raya gabobi 2 na mashigin, ta yadda za a kyautata walwalar daukacin Sinawa na gabobin 2 na mashigin Taiwan na kasar Sin.

Rahoton ya nuna cewa, kasar za ta zurfafa hade dabarun raya masana’antu masu tasowa bisa manyan tsare-tsare da sauran dimbin kokarin karfafa ci gaban wadanda za a kafa nan gaba.

Rahoton aikin ya ce, kasar Sin za ta aiwatar da shirye-shiryen nuna yadda za a yi amfani da manyan sabbin fasahohi, da kayayyaki da tsare-tsaren ciyar da al’amura gaba, da matsa kaimi ga bunkasa harkokin kasuwanci cikin aminci da inganci, da tattalin arzikin kananan jirage masu tashi kasa-kasa, da sauran masana’antu masu tasowa.

Har ila yau, rahoton ya ce, kasar za ta bullo da hanyar da za ta kara samar da kudade ga masana’antun da za a kafa nan gaba da kuma karfafa ci gaban masana’antu kamar na sarrafa halittu, da fasahar daidaita makamashi ta ‘quantum’, da fasahar kere-keren kirkirarriyar basira AI, da kuma fasahar sadarwa ta 6G.

A cewar rahoton, kasar Sin za ta ba da goyon baya ga bunkasa kanana da matsakaitan kamfanoni masu zaman kansu a shekarar 2025, inda ya kara da cewa, kasar za ta ci gaba da zurfafa raya sana’o’in kirkire-kirkire, da inganta ci gaban kanana da matsakaitan masana’antu da ke amfani da fasahohin zamani na musamman domin samar da sabbin kayayyaki da za su kasance daban da na saura.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin za ta kasar za ta

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete

Maryam Abubakar, ɗaya ce daga cikin jaruman masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood ’yan ƙalilan da suka yi nasarar bin sahun iyayensu a harkar fim.

Matashiyar jarumar, wadda aka fi sanin ta da Maryam Intete a masana’antar, ta yi bayani a kan matsayinta na wadda iyayenta suka suka a cikin cikin harkar fim.

Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A wannan tattaunawar, jarumar ta yi bayani game da gogewarta da yadda ake samun daukaka a Kannywood, da wasu abubuwa game da ita kanta da iyayenta, da kuma sana’ar fim da dai sauransu.

Wace ce Maryam Abubakar?

An haife ni ne a Kano kuma a nan na girma. Na yi makarantar firamare da sakandare duk a Kano, daga baya na koma kasar Saudiyya inda na yi shekaru masu yawa a can.

Bayan na dawo Nijeriya ne na shiga harkar wasan fim kamar yadda na riski mahaifiyata na yi.

Ina da shekaru sama da ashirin, dangina na daga cikin masu shirya fina-finai a masana’antar Kannywood.

Idan mutum zai iya cewa sana’ar fim tana gudana a jininsa, to zan iya cewa fim na gudana a jinina, domin mahaifina ya dan yi aiki a masana’antar Kannywood kafin ya daina.

Mahaifiyata kuma har yandu tana ci gaba da taka rawa sosai a harkar shirya fina-finan Hausa.

Wanann ne ya sa na ce wasan kwaikwayo yana gudana a cikin jinina.

Amma duk da haka, ban taba tunani zama ’yar fim ba duk da cewa na kasance wani bangare na rayuwata a cikin harkar ta ginu.

Abin mamaki, bayan dawowata daga Saudiyya, na fara sha’awar bin sahun iyayena a sana’ar tasu.

Ko za ki iya mana karin bayani a kan su waye iyayenki da kika ce suna harkar fim?

Kamar yadda na faɗa a baya, mahaifina ya ɗan yi aiki a masan’antar amma mutane da yawa ba za su iya tunawa da shi ba ko da na ambaci sunansa.

Mahaifiyata kuma ta kasance ginshiki mai karfi a tarihin Kannywood, har yanzu tana taka rawa sosai a masana’antar domin tarihin masana’antar fina-finan Hausa ba zai cika ba sai an ambaci sunanta da kuma rawar da ta taka wajen ci gaban masana’antar.

Ba wata ba ce illa malama Hauwa Garba wadda aka fi sani da ’Yar Auta ko Sabura a cikin shirin Gidan Badamasi.

Ni ’yarta ce kuma ko ku yarda ko kar ku yarda nagartar mahaifiyata ce ta ja ni Kanywood.

Ana girmama ni saboda kasancewarta ’yarta kuma duk sauran ’yan wasan da na hadu da su a masana’antar a shirye suke su ba ni duk wata gudummawa da goyon baya da nake bukata.

Tun yaushe kike masana’antar Kannywood?

Yanzu dai na yi fiye da shekara biyu, kuma abin al’ajabi da sha’awa, shi ne, a cikin wannan ɗan gajeren lokaci, na yi fina-finai da yawa kuma na taka rawa a cikin kusan finafinai hudu.

Haka kuma, masu shirya fina-finai a kodayaushe suna son su saka ni a finafinansu musamman idan sun fahimci cewa ni ’yar Yar Auta ce.

Bayan fina-finan da na fito a ciki, ina da sauran fina-finan da ke jira na.

Dole ne in nuna godiya ta kwarai ga furodusoshin Kannywood bisa yadda suka amince da kuma yarda da iya wasana, dole kuma in yaba wa mahaifiyata saboda ta saukaka min tafiya, ta hanyar zama abin koyi ga yawancin matasa masu basira.

Yaya za ki kwatanta ranarki ta farko a gaban kyamara?

Ko da yake ba bakon abu ba ne a gare ni, amma bai kasance mai sauki kamar yadda nake tsammani zai kasance ba.

Idan za ka iya tunawa na gaya maka cewa na taso ne a cikin dangi inda wasan kwaikwayo ya bunkasa kuma don haka na san duk abubuwan da ke ciki.

Amma ba kamar yadda nake tunani ba, rana ta farko ta tabbatar mini da cewa akwai abubuwa da yawa fiye da abin da muke tsammanin harkar fim ta kunsa.

Abun burgewa shi ne kowa a shirye yake ya taimaka min kuma ya karfafa min gwiwa domin yin nasara.

Mene ne ra’ayin mahaifiyarki yayin da kika so shiga Kannywood?

Maganganun mahaifiyata su suke kara min karfin gwiwa wajen yin gaba kuma ina ganin tasirinsu a cikin tafiyata.

Ta ce da ni, “Maryam dole ne ki girmama kowa a wannan masana’antar, su ne manyanki kuma su ma za su yi miki jagora, ki tuna fa abokan aikin mahaifiyarki ne.”

“Wannan shi ne sirrina, ina mutunta kowa da kowa a masana’antar, kuma duk sun kasance kamar dangi ne a gare ni.

Za ki iya fitowa cikin fim daya tare da mahaifiyarki?

Fitowa a fim ɗaya tare da mahaifiyata abin alfahari ne gare ni, fim shi ne sana’ar da muke yi don dogaro da kanmu, mahaifiyata ta shahara a Kannywood kuma tana da dabi’u masu kyau, da suka cancanci a yi koyi da ita.

Kowa a masana’antar yana girmama ta saboda rawar da take takawa a duk shirin da aka saka ta.

Zan iya cewa fitowata a fim daya tare da ita zai zamo abin alfahari a matsayina na jaruma, dama ce a gare ni wacce ba kowa yake da ita ba.

Babbar nasara ce a gare ni shigowata cikin masana’antar Kannywood tun mahaifiyata tana taka rawar gani a cikinta.

Wanne abu ne ba za ki taɓa mantawa ba a matsayinki na jaruma?

Abin da ba zan taɓa mantawa ba a matsayina na jaruma shi ne duk lokacin da mutane suka nuna sun san ni a matsayin ’yar ’Yar Auta.

Girmamawa da kuma nuna sanayya da suke min a matsayin ’yarta abu ne da nake kauna wanda ba zan taba mantawa da shi ba a rayuwata.

Hakan ya nuna cewa mahaifiyata shahararriya ce, ta yi shuhura sosai a duniya, ta kafa kyakkyawan tarihi da hakan ke bin ’yayanta.

Kina da shirin da kike aikinsa a halin yandu?

Eh, ina aiki a kan shirin talabijin mai dogon zango mai suna ‘Baban Yawa’, kuma kamar yadda na faɗa a baya, ina da wasu ayyuka da ke jira na, amma a yanzu ina aiki a kan shirin mai dogon zango ne kawai.

Shin Maryam tana soyayya?

A gaskiya ba na yin soyayya. Babban abin da na sa a gaba shi ne na yi shuhura a cikin masana’antar, daga baya kuma sauran wasu abubuwa su biyo baya.

Za ki ci gaba da harkar Kannywood bayan kin yi aure?

A’a, ba na tunanin ci gaba, duk lokacin da na yi aure to na bar harkar fim a Kannywood ke nan.

Mece ce shawararki ga masu tasowa a Kannywood?

Su girmama kowa, ba da yawan fina-finai da ka fito ake samun ɗaukaka ba, shahara ita ce yawan mutane da kuka yi hulɗa da su ta hanyar wasan kwaikwayo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • Hanyoyin da za a magance rikicin Filato — Masana