Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa
Published: 5th, March 2025 GMT
Fa’iza Muhammad wacce aka fi sani da Fa’iza Badawa, daya ce daga cikin mawakan Kannwood.
Ita ta yi wakar fim din Oga Abuja, daya daga cikin finafinan suka yi tashe, ya kuma fito da basirar mawakiyar.
Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-giluKasancewar ta yi aure, mutane sun ɗauka ta daina harkar waƙa baki ɗaya.
Yaushe kika yi aure?
Na yi aure ne a ranar 8 watan Afrilun shekar 2017, kuma ina zaune lafiya da mijina da kuma haihuwa daay da Allah Ya bamu, kuma aure ne na so ada kauna da kuma kyakkyawar kulawa. Kuma yana taimaka min tare da goya min baya a abubuwan ada na ke yi.
Shin gaskiya ne cewa auren ne ya hana ki ci gaba da waka?
Ba gaskiya ba ne. Har yanzu ina yin waka, kuma duk wasu manya-manya da ke wannan sana’a sun san har yanzu ina yin waka saboda muna aiki tare.
Duk lokacin da suke bukatar aiki da ni, su kan kira ni ko kuma su kira mijina tare neman izininsa na mu yi aiki ko aika masa sako zuwa gare ni.
Mu mawaka a bayan fage muke, ba ganinmu ake yi ba, sai dai a ji muryoyinmu wanda da shi a ke gane mu, da kuma cewa, yawancinmu mawaka mata da zarar mun yi aure sai mu daina aiki, shi ya sa da yawa suka dauka nima na daina waka.
A lokuta na kan yi wa abokan aikina bayani cewa, ina nan, na kuma ci gaba da sana’ata ta waka a wannnan masana’antar tamu.
Shin ko yaya ki ke tafiyar da wannan sana’a a yanzu da kina matar aure?
Wani tsari na fito da shi la’akari da tsarin addinina da kuma kula da matsayina a inda na kan bukaci duk mai son in yi mi shi waka da ya je ya gama rubuta wakarsa, ya kuma gama shiririnsa da wurin daukar murya.
Idan ya yi hakan, sai in nemi a sa min ranata ni kadai da zan je in yi nawa baitukan ko kuma dora murya. Inda na gama sai su ci gaba da sauran wadanda za su yi da su.
Kuma ya kamata ka sani cewa, ba ni kadai ce na ke da aure ba, na kuma ke waka, domin muna da yawa a yanzu fiye da yadda ka ke tunani.
Ka ga da akwai Zuwairiya Isma’ila, da Murja Baba, da Naja’atu Ta’Annabi, da Maryam A Baba, da Jamila Sadi, da Zainab Diamond, da Sa’a Bocal, da kuma Sa’a Nazifi Asnanic. Da sauransu.
Wane kalubale ne kike fuskanta a matsayinki na mawakiya kuma matar aure?
Ni babu wata matsala da na ke fuskanta a matsayina na matar aure kuma mai sana’ar waƙa musamman ma a gidan mijina.
Domin akwai kyakkyawar fahimta tsakanina da shi, bayan so da kauna, ya na bani sharwari tare da tallafa min a duk al’amurana ciki har da wannan sana’a ta waka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fa iza Badawa kannywood Waƙa
এছাড়াও পড়ুন:
Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
Hukumomin kasar za su fitar da gamsasshen bayani mai dauke da sababbin tsauraran matakan, wadanda za su kunshi na mallakar izinin karatu da aiki a Birtaniya.
Sakataren harkokin baki na Birtaniya Ybette Cooper ta bayyana wa BBC cewa lokaci ya yi da za su rage daukar ma’aikatan jinya daga kasashen waje.
Ta ce wannan matakin zai taimaka wajen rage kusan mutum 50,000 wadanda ba kwararru ba ne sosai da suke shiga kasar daga kasashen ketare a duk shekara.
Firaministan ya ce sababbin matakan za su taimaka wajen “sake mallake bakin iyakokin kasarmu.”
Idan aka dabbaka sabbin matakan nan da gwamnatin kasar za ta dauka, ‘yan kasashen mutane daga kasashen Nijeriya da Pakistan da Sri Lanka za su fuskanci kalubale wajen samun izinin shiga kasar Birtaniya domin karatu.
Abin da hakan ke nufi
Starmer ya ce Birtaniya za ta rika neman wadanda suka fi kwarewa ne a duniya wajen daukar aiki, sannan za su bincika me ya sa wani bangaren aikin kasar ya fi mayar da hanakali kan “neman sauki wajen daukar aiki.”
Firaministan ya ce sabbin matakan za su fayyace komai da komai game da tsare-tsaren shige da fice a kasar – iyali da karatu da aiki.
“Zan tabbatar da matakan nan saboda za su tabbatar da adalci, kuma abin da ya dace ke nan,” in ji Starmer a wani taron manema labarai.
Ya ce bai kamata a rika mayar da hankali kan neman sauki wajen daukar ma’aikata ba, maimakon mayar da hankali kan horar da matasan kasar.
Starmer ya kara da cewa bakin da suke shigowa kasar a gwamnatin baya sun kai kusan miliyan 1 a shekarar 2023, wanda shi ne adadi mafi yawa.
Ya ce adadin bakin ya kai adadin mutanen birnin Birmingham baki daya, wanda kuma shi ne birni na biyu mafi girma a Birtaniya.
“Wannan ba ci gaba ba ne, kasada ce. Ba zai yiwu a ce da kuskure hakan ya faru ba, wannan ganganci aka yi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp