Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe
Published: 5th, March 2025 GMT
Wata mummunar gobara ta ƙone shaguna sama da 17 a ɓangaren ’yan teloli da masu hada-hadar kayan abinci a tsohuwar kasuwar garin Gombe.
Gobarar, wadda ta fara da misalin ƙarfe 2:00 na dare, ta jefa ’yan kasuwa cikin jimamin asarar dukiya mai tarin yawa da aka kiyasta ta kai miliyoyin naira.
Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurataWasu da lamarin ya faru a kan idonsu, sun bayyana cewa gobarar ta bazu cikin sauri, inda ta riƙa laƙume kaya da kadarori kafin ’yan kwana-kwana su iso wurin.
Ko da yake ba a tabbatar da musabbabin tashin gobarar ba, amma wasu ’yan kasuwar na zargin cewa matsalar wutar lantarki ce ta haddasa ta.
Wani daga cikin ’yan kasuwar da lamarin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana bakin cikinsa da cewa, “Mun rasa komai.
“Mutanenmu da dama sun saro kaya a kwanan nan, amma yanzu duk sun ƙone. Wannan babban kalubale ne a gare mu.”
Wakilinmu ya ruwaito cewa jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Gombe tare da gudunmawar wasu mazauna ne suka taimaka wajen hana gobarar bazuwa zuwa wasu sassan kasuwar.
Sai dai, kafin a kashe gobarar gaba ɗaya, tuni ta riga ta yi mummunar ɓarna.
Har yanzu mahukunta ba su fitar da wata sanarwa game da lamarin ba, sai dai shugabannin ’yan kasuwa suna kira ga gwamnati da ta taimaka wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.
Sun kuma yi kira da a ɗauki tsauraran matakan daƙile gobara don hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.
Wannan gobarar ta shiga jerin gobarar da suka auku a kasuwannin Gombe a cikin ’yan shekarun nan, lamarin da ya jaddada muhimmancin samar da ingantattun matakan daƙile aukuwarta a wuraren kasuwanci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara jihar Gombe kasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza
Babban jami’in bada agaji na Majalisar Dinkin Duniya ya kira matakin da Isra’ila ta dauka na dakatar da agajin dake shiga Gaza a matsayin abin damuwa.
Jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher, ya yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na katse taimakon da take baiwa Gaza, yana mai cewa abin takaici ne.
A wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, ya tuna cewa “Dokar kasa da kasa ta bayyana karara cewa dole ne a bar agajin jin kai ya shiga zirin Gaza.”
Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da dama da kwararru kan kare hakkin bil adama sun yi gargadin cewa wannan mataki ya zama keta dokokin kasa da kasa da kuma tauye hakkin bil’adama.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Norway (NRC) ta jaddada cewa dakatar da tallafin da Isra’ila ke yi gaba daya zai haifar da mummunan sakamako ga fararen hula fiye da miliyan biyu da tuni ke fuskantar yunwa.
“Taimakon jin kai ba gata ba ne, hakki ne,” in ji Angelita Caredda, darektan yankin NRC na Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka.
A halin da ake ciki, kungiyar likitoci marar iyaka (MSF) ta yi kakkausar suka ga Isra’ila saboda amfani da agajin jin kai a matsayin makami.
“Bai kamata a yi amfani da taimakon jin kai a matsayin makamin yaki ba,” in ji kungiyar agaji ta likitoci ta kasa da kasa.