’Yan sanda sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Gombe
Published: 5th, March 2025 GMT
’Yan sanda sun ceto wani mutum mai shekaru 48, Alhaji Samaila Muhammed, da aka yi garkuwa da shi a ƙauyen Lano da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba ta Jihar Gombe.
An gudanar da aikin ceton bisa tsari tare da haɗin gwiwar ‘yan banga na yankin, lamarin da ya tabbatar da cewa mutumin ya shaƙi iskar ’yanci salin-alin.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, mahukunta sun tabbatar da ƙoshin lafiyarsa sannan daga bisani aka sada shi da ’yan uwansa.
Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.
DSP Buhari ya tabbatar wa jama’a cewa za a ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ayyukan laifi a jihar.
Sanarwar ta kuma gode wa jama’a bisa haɗin kansu tare da yin kira da su kasance masu sa ido, su kuma riƙa sanar da hukuma game da duk wani abu da suka ga ya dace ko ya saɓa da al’ada a cikin al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane jihar Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
Lin Jian Ya Yi Bayani Kan Takardar Bayani Game Da Shawo Kan Sinadarai Masu Alaka Da Sinadarin Fentanyl Ta Sin
A ranar 4 ga wata, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya fitar da takardar bayani game da shawo kan sinadarai masu alaka da sinadarin Fentanyl. Takardar ta yi cikakken bayani kan yadda kasar Sin ta gudanar da aikin shawo kan bazuwar sinadarai dangin Fentanyl, da nasarorin da ta cimma, yayin da gabatar da fasahohin kasar Sin wajen gudanar da ayyukan da abin ya shafa.
Dangane da wannan takardar da kasar Sin ta fidda, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana cewa, takardar za ta ba da taimako ga al’ummomi da gamayyar kasa da kasa wajen kara musu fahimtar matsayin kasar Sin kan wannan batu, da matakan da Sin ta dauka, da kuma nasarorin da Sin ta cimma a wannan fanni. Kasar Amurka ta yada jita-jita kan batun Fentanyl domin bata sunan kasar Sin, tare da kara haraji kan hajojin kasar Sin bisa wannan hujja. Babu sanin ya kamata cikin wannan lamarin. Amurka ta cutar da wasu da kai karan kanta.
Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin JiangsuA sa’i daya kuma, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen habaka hadin gwiwar dake tsakaninta da Amurka bisa ka’idar nuna adalci da girmama juna, kuma tana adawa da dukkan irin matakan da Amurka ta dauka domin matsa wa kasar Sin lamba, bisa hujjar batun Fentanyl. Sin ta bukaci Amurka da ta mutunta gaskiya, da kare moriyar kanta yadda ya kamata, domin gudanar da harkoki ta hanyoyi masu dacewa.
Lin Jian ya kara da cewa, Amurka ta sake kara haraji kan hajojin Sin bisa hujjar batun Fentanyl, kana, sau da dama, kasar Sin ta nuna adawa kan wannan batu. Dukkanin matakan mayar da martani da kasar Sin ta dauka sun kasance matakan da suka wajaba kuma masu dacewa domin kare moriyar kasa. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp