Leadership News Hausa:
2025-04-25@18:01:21 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Published: 5th, March 2025 GMT

Matar Aure Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta A Bauchi

Tunin Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad ya umarci babban baturen ɗansanda a C Division da ya jagoranci tawaga ta musamman da za su gudanar da bincike kan lamarin a tsanake.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar, yunkurinsu a halin yanzu ya kai ga kama Fatima Mohammed, kishiya ga mamaciyar wacce a halin yanzu take tsare a hannunsu.

“Bincike na farko ya nuna cewa, akwai zargin Fatima Mohammed na da hannu a mutuwar Hajara. A yayin da ake yi mata tambayoyi, an ce ta amince ta shaƙe ta har lahira, sannan ta yi yunƙurin ɓoye laifin ta hanyar zuba mata tafasasshen ruwa tare da ƙona jikinta da buhun da ke narkewa,” in ji CSP Wakil

A sanarwar, rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da aniyarta na wanzar da adalci a kowani lokaci, inda ta ce za a mayar da kes ɗin zuwa sashin kula da manyan laifuka SCID.

Wakil ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yansandan jihar ya umarci tawagar kwararru da su hanzarta tattara bayanan da suka shafi wannan mutuwar ciki har da zarge-zarge da ake yi kan mutuwar Hajaran.

CP Auwal ya hori jama’an binciken da su gaggauta gudanar da bincike su tare da aiki da kwarewa inda ya tabbatar da cewa za su yi ƙoƙarin wanzar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Binciken Ƙwaƙwaf Kan Yaddda NNPCL Ke Hada-hadar Kuɗaɗensa – Ministan Kuɗi

“Akwai wasu bincike da ake gudanarwa domin kamar yadda muka sani, an sanar da cire tallafin man fetur ne a ranar 29 ga watan Mayun 2023, amma an dauki lokaci kafin a cimma wannan kudurin. A halin yanzu, wani bangare na biyan basussukan da ake bin NNPC, daga kasafin kudin gwamnati ake tanada”.

 

Ya kara da cewa, babban aikin da ke gaban NNPCL shi ne bunkasa hako danyen mai da kuma samar da karin kudaden shiga – a takardun Dala zuwa Asusun Tarayya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Iran Ta Musanta Zargin Nethalands Na Cewa Tana Da Hannun A Kokarin Kisa A Kasar
  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • An Fara Binciken Ƙwaƙwaf Kan Yaddda NNPCL Ke Hada-hadar Kuɗaɗensa – Ministan Kuɗi
  • Ƙasurgumin Ɗan Fashin Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Mutu Bayan Arangama Da ‘Yansanda A Kano
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi