HausaTv:
2025-04-25@15:13:20 GMT

Kungiyar Hamas Ta Ki Amincewa Da Kwance Damarar Kungiyar A Gaza

Published: 5th, March 2025 GMT

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ya yi watsi da bukatar HKI na kwance damarar dakarun kungiyan a matsayin sharadi na ci gaba da aiwatar da yarjeniyar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Kungiyar ta kara da cewa, kwance damara dakarun kungiyar jar layi ne a wajenta.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI tana bukatar ta raba kungiyar da makamanta, kafin ta ci gaba da aiwatar da yarjeniyar ta watan Jeneru.

Wannan  bukatar dai ta sa tababa a cikin yiyuwar tsagaita wuta tsakanin HKI da Hamas ya dore.

Yarjeniya ta yanzu dai, wacce ta faraaiki a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025, kuma an tsara shi bisa marhaloli 3. Daga ciki har da tsarin yadda masu shiga tsakani zasu gabatar da musayar fursinoni da har zuwa janyewar sojojin HKI daga Gaza. Amma gwamnatin Natanyahu tace ba zata taba ficcewa daga Gaza ba.

Kakakin kungiyar Sami Abu Zuhri ya ce: Batun kwance damarar dakarun Izzudden Qassam, maganar banza ce. Makaman hamas jar laye ce, wand aba zata taba amincea da haka. Ministan harkokin wajen HKI, Gidion Sa’ar ya ce: Muna bukatar kwance damarar Hamasa da Jihadul Islamu da sauransu, sannan a mika mana yahudawan da ake garkuwa da su, idan sun yi haka, gobe ma a aiwatar da yarjeniyar.

Sannan wani kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem yace Hamas ba za ta amince da tsawaita marhala ta farko na yarjeniyar ba. Ya kuma bukaci a takurawa HKI don ta amince da ci gaba da aiwatar da marhaloli na gaba.

Natanyahu ya dauki yarjeniyar a matsayin na wucin gadi ne, don haka za’a iya komawa yaki a ko wani lokaci. A cikin makonni masu zuwa ne zamu gane, kan cewa, yarjeniyar zata ci gaba ko kuma za’a koma yaki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a aiwatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Sojan HKI Ya Halaka A Gaza

Kafafen watsa labarun HKi sun amabci cewa daya daga cikin sojojinsu ya halaka a Gaza, yayin da wasu 7 su ka jikkata.

Kafafen watsa labarun na HKI sun ce, Harin da aka kai wa sojojin ya kunshi harbi daga kwararren maharbi da kuma harba makamin dake fasa motoci masu sulke.

An ga jiragen sojan mamaya suna tsananta hare-hare a yankin da lamarin ya faru, saboda su sami damar dauki gawar sojan nasu da kuma wadanda su ka jikkata.

Tashar talabijin ta 12; ta HKI ta ambaci cewa;Ana gwabza fada ne a arewacin Gaza, kuma mazauna yankin suna cewa sun ga jiragen sama masu yawa suna kai da komo.

 Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare masu yawa a yankin Arewacin Gaza, kamar kuma yadda wata kafar ta ce an ji karar fashewar wasu abubuwa da karfi a cikin yankin Naqab ta yamma.

A wani labarin daga Gaza, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada a yau kadai sun kai 56.

Jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a yankunan Arewan yammacin Gaza da kuma Jabaliya da shi ne musabbabin shahadar adadi mai yaw ana Falasdinawan a yau.

A Jabaliya kadai jiragen yakin HKI sun kai hari ne akan wani gida da ‘yan hijira suke cikinsa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 15.

A Arewacin Gaza kuwa mutane an sami shahidai 39, sai kuma wasu 7 da su ka jikkata a cikin birnin Gaza kamar yadda kamfanin dillancin labarun “Anatoli” ta Turkiya ya nakalto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • ICC ta ki amincewa da bukatar Isra’ila na soke sammacin kama Netanyahu
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Aniyar Kasarsa Ta Goyon Bayan Kudurorin Kyautata Yanayi Da Ci Gaba Marar Gurbata Muhalli
  • Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba
  • Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso