Iran Ta Ce Dole Ne Amurka Ta Janye Mata Takunkuman Tattalin Arziki Masu Gurgurtawa Da Ta Dora Mata
Published: 5th, March 2025 GMT
Mataimakin ministan harkokin wajen a kan al-amuran siyasa, dole ne Amurka ta daukewa kasarsa wadannan takunkuman tattalin arziki wanda suke cutar da mutanen kasar Iran da al-adunsa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto TakhtaRawanchi yana fadar haka a shafinsa na X ko twitter a da, a kuma jiya Talata, Mataimakin ministan ya kara da cewa, takunkuman tattalin arzikin da kasashen Amurka da Turai suka dorawa kasar Iran ya zuwa yanzu ya shafi rayuwar mutanen kasar da dama wanda kuma take hakkinsu ne.
Labarin ya kara da cewa a shekaru fiye da 40 da suka gabata, gwamnatocin Amurka kadai sundorawa kasar Iran takunkuman tattalin arziki mafi muni, kuma nau’ii daban-daban. Haka ma ta dade tana wa kasar barazanar far mata da yaki, takunkuman tattalin arziki mafi muna, yakin farfaganda na kasya da sauransu.
Duk da cewa gwamnatocin kasar ta Amurka sun kasa cimma manufofinsu na dorawa kasar ta Iran takunkuman tattalin arziki, Washington ta ci gaba da dorawa kasar wadannan takunkuman tattalin arziki. Duk da cewa hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: takunkuman tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: An Bukaci Kasa Da Kasa Su Bijirewa Cin Zali Daga Amurka
Nemi adalci maimakon babakere. Cin zali ta hanyar kakaba haraji da Amurka ke yi, ya haifar da suka da adawa da martani daga kasashe da dama. Takarda mai dauke da matsayar kasar Sin da aka fitar dangane da cin zalin ta samu goyon bayan daga kasa da kasa. Sakamakon wani nazari da kafar CGTN ta gudanar tsakanin masu amfani da intanet a fadin duniya, ya nuna wadanda suka amsa nazarin na kira ga kasashen duniya su hada hannu su dauki mataki domin bijirewa salon cin zali irin na Amurka, su kare hakkokinsu da kuma tsarin cinikayya da tattalin arziki na duniya.
Bisa fakewa da daidaito da adalci, Amurka na son cin riba daga faduwar wasu, inda take sanya muradunta sama da na al’ummar duniya. Kasar Sin na adawa da hakan tana mai bayyana neman ci gaba a matsayin ‘yanci na bai daya na dukkan kasashe ba na wasu ‘yan tsiraru ba.
Game da hakan, kaso 86.9 na masu bayar da amsa sun yi ammana cewa, matakan martani da kasashe suka dauka game da matakan Amurka na cin zali ta hanyar haraji, abu ne da ya halatta na kare muradunsu. Har ila yau, kaso 89.2 sun yi kira ga karin kasashe su dauki karin matakai na kandagarki game da batutuwan cinikayya da Amurka, suna masu bayyana adawa da yadda Amurka ke yin gaban kanta wajen cin zali a dandalin hadin gwiwar kasa da kasa kamar hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO). (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp