Ban taɓa cin zarafin Natasha ba, ina girmama mata — Akpabio
Published: 5th, March 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya nesanta kansa daga zargin cin zarafin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda ya ce mahaifiyarsa ta ba shi tarbiyya mai kyau, kuma yana mutunta mata.
Akpabio ya bayyana hakan ne bayan da Sanata Natasha ta zarge shi da cin zarafinta ta hanyar neman kwanciya da ita, wanda ya haifar da rikici a zauren majalisa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: “Ina son duniya ta sani cewa ban taba cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace ba. Mahaifiyata ta yi min tarbiyya mai kyau, ina girmama mata.”
Wannan bayani na Akpabio ya zo ne a yayin da ake ta cece-kuce kan rikicinsa da Sanata Natasha, wanda ya samo asali daga zargin da ta yi masa kan wasu abubuwa da suka faru a baya.
Rikicin ya ɗauki sabon salo a zauren majalisar bayan da aka buƙaci ta sauya wajen zama, wanda ta ƙi amincewa da shi.
A zaman majalisar na baya, Sanata Natasha ta tsaya kai da fata tana kare kanta, inda ta nuna rashin amincewarta da matsin lamba da ta ke fuskanta.
Wannan ya jawo ruɗani a majalisar har aka buƙaci jami’an tsaro su fitar da ita daga zauren.
Sai dai, a cikin bayaninsa, Akpabio ya ce ba ya gaba da Sanata Natasha, kuma yana girmama mata a kowane hali.
Ya ce: “Tun daga yarinta, an koya min daraja mata, kuma a matsayina na jagora, ba zan taɓa nuna wariya ko cin zarafi ga kowace mace ba.”
A yanzu, jama’a na ci gaba da bibiyar wannan rikici don ganin yadda za a warware shi, yayin da ‘yan majalisa ke ƙoƙarin shawo kan lamarin domin kada rikicin ya ƙara ta’azzara a cikin majalisar dattawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Ruaɗani zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
Wasu mutane 13 sun faɗa a komar ’yan sanda ka zargi da zubar da ciki da kuma mutuwar wata budurwa ’yar shekara 18 a Jihar Bauchi.
Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya ce ana tuhumar huɗu daga cikin mutanen da aikata laifin fyade, zubar da ciki da kuma mutuwar budurwa a garin Misau da ke Ƙaramar Hukumar Misau.
Wakil ya ce, a ranar 4 ga Afrilu, 2025 sun samu bayanai ewa, kimanin watanni hudu da suka gabata, wasu matasa biyu a yankin Lariski da ke Misau, sun kama wata yarinya mai shekaru 18 da suka yi ta yi lalata da ita sau da yawa.
Ya ce a lokacin da suka lura tana ɗauke da juna biyu, sai suka nemi wani mutum suka ba shi naira 40,000 don ya taimaka musu wajen zubar da cikin, amma abin takaici sai aka samu matsala wanda a qarshe ya yi sanadiyyar mutuwarta.
Wakil ya ce, “Bayan an yi mata allurar zubar da ciki saita fita daga hayyacinta, daga baya kuma ta kamu da rashin lafiya. Hakan ya sa danginta suka kai ta Babban Asibitin Misau, daga baya an mika ta zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (FMC) da ke Azare, inda hukumomin asibitin suka sanar da cewa ta mutu a lokacin da take jinya.”
Bayan samun rahoton, an kama wadanda ake zargin, inda suka amsa laifin da suka aikata tare da ambaton wasu da ke da hannu a lamarin. Ya ce sauran wadanda ake zargin da wasu mutum huɗu suna hannun ’yan sanda ana bincike.
Bayan haka kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya bisa laifukan da suka aikata.”