Aminiya:
2025-05-06@06:46:27 GMT

Zargin Cin Zarafi: Natasha ta gabatar wa majalisa ƙorafinta game da Akpabio

Published: 5th, March 2025 GMT

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, ta gabatar da ƙorafinta a gaban Majalisar Dattawa kan Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, bisa zargin cin zarafi da kuma tauye mata haƙƙi a majalisa.

A ranar 20 ga watan Fabrairu ne rikici ya ɓarke a zauren majalisar, lokacin da Shugaban Majalisar, Akpabio, ya umarci wani ma’aikacin majalisa da ya fitar da Sanata Natasha daga zauren, bayan da aka ce ta ƙi komawa sabuwar kujerar da aka ware mata.

Matashi ya hallaka mahaifiyarsa da duka a Bauchi Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe

Wannan lamarin ya jawo suka daga ƙungiyoyi da mutane da dama, inda suka nemi a yi bincike kan abin da ya faru.

Abin da Sanata Natasha Ta Gabatar Wa Majalisa

Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafinta ga Majalisar Dattawa, inda ta ce: ’Ina gabatar da ƙorafi kan Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, bisa cin zarafi na lalata da kuma amfani da muƙaminsa wajen tauye min haƙƙi na ’yar majalisa.”

Daga nan sai ta sauka daga kujerarta zuwa gaban Akpabio, inda ta rusuna sannan ta ajiye takardun ƙorafinta.

Shugaban Majalisar, Sanata Akpabio, ya karɓi ƙorafin, inda ya miƙa shi ga Kwamitin Ladabtarwa da Tsare-Tsare domin gudanar da bincike.

Ya ce: “Na miƙa wannan ƙorafi ga kwamitin ladabtarwa na majalisar dattawa domin yin bincike kuma su dawo mana da rahoto cikin gaggawa.”

Duk da haka, yayin da ake tattaunawa, Babban Mai Tsawatarwa na Majalisa, Sanata Mohammed Monguno, ya ce ba za a iya tattauna ƙorafin ba saboda yana da nasaba da shari’ar da ke gaban kotu.

Sai dai Sanata Natasha ta musanta hakan, inda ta bayyana cewa ƙarar da ake yi a kotu ba ta shafi ƙorafin da ta gabatar ba.

Ta bayyana cewa abin da ke gaban kotu na da nasaba da wani hadimin Akpabio, Patrick Mfon, wanda ya zarge ta da sanya kayan wanda ba su dace ba a majalisar.

Martanin Sanata Akpabio

Bayan karɓar ƙorafin, Akpabio ya musanta duk wasu zarge-zarge da Natasha ta yi masa.

Ya ce: “Dangane da zargin da ake yi min, babu lokacin da na taɓa yunƙurin cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace.

“Mahaifiyarmu ta ba mu tarbiyya tun muna ƙanana, kuma ni ma ina da ’ya’ya mata huɗu. Bugu da ƙari, lokacin da nake gwamna, an taɓa karrama ni a matsayin gwamnan da ya fi kowa girmama mata.”

Akpabio ya kuma jaddada cewa lamarin na gaban kotu, don haka ya buƙaci kafafen watsa labarai da al’ummar Najeriya su jira sakamakon shari’a.

Sanata Natasha Ba Ta Samu Goyon Bayan ’Yan Majalisa Ba

Bayan gabatar da ƙorafin, mafi yawancin ’yan majalisar dattawa da suka yi tsokaci ba su goyi bayan Natasha ba, har da sanatoci mata ’yan uwanta.

Wasu daga cikinsu sun ce ƙorafin ba shi da tushe, don haka bai kamata a tattauna shi a zauren majalisar ba.

Wasu kuma sun nemi a yi zaman sirri domin tattauna lamarin, amma Akpabio ya ƙi amincewa da hakan saboda akwai baƙo da ya ziyarci majalisar daga Birtaniya, wanda ke kallon yadda zaman majalisar ke gudana.

Daga ƙarshe, yayin da ’yan majalisar suka ci gaba da aikinsu, Sanata Natasha ta fice daga zauren majalisar domin nuna rashin jin daɗinta da yadda lamarin ya kaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamiti Ƙorafi Majalisar Dattawa Zargin Cin Zarafi Shugaban Majalisar gaban Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Bankin AfDB zai zuba jarin $650m a Nijeriya a duk shekara

Bankin Raya kasashen Afirka (AfDB) ya ware dala miliyan 650 a duk shekara tun daga 2025 zuwa 2030 domin wani shiri na musamman na habaka ci gaban tattalin arziki a Nijeriya.

Bankin ya sanar da hakan ne a wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce za a samar da dala biliyan 2.95 tsawon shekara hudu a wannan shirin, inda zai samu ƙarin kimanin dala biliyan 3.21 daga sauran ƙawayen kawo ci gaba.

Sanarwar ta ce shirin zai mayar da hankali kan abubuwa biyu muhimmai wadanda suka hada da kawo ci gaba ma dorewa da samar da ababen more rayuwa wadanda suka zo daidai da tsarin da ake da shi na sauyin yanayi da samar da gasa da ci gaban masana’antu; da kuma samar da daidaito a tsakanin matasa da jinsi ta bangaren ci gaban masana’antu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sha Alwashin Mayar Da Martani Cikin Gaggawa Kan Duk Wani Hari Kan Kasarta
  • Majalisar Kano Ta Amince Da Dokar Wutar Lantarki Da Za Ta Raba Wa Jihohi 3 Wuta
  • Yadda ’yan fashi suka yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi
  • ’Yan fashi sun yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi
  • Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
  • ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe 
  • Bankin AfDB zai zuba jarin $650m a Nijeriya a duk shekara