Aminiya:
2025-04-05@09:43:59 GMT

Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio

Published: 5th, March 2025 GMT

Kwamitin Ladabtarwa da Ɗa’a na Majalisar Dattawa, ya yi watsi da ƙorafin da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ta shigar kan Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, inda ta zarge shi da cin zarafinta.

Kwamitin ya bayyana ƙorafin a matsayin “mattacen ƙorafi tun kafin a duba shi.”

Zargin Cin Zarafi: Natasha ta gabatar wa majalisa ƙorafinta game da Akpabio Matashi ya hallaka mahaifiyarsa da duka a Bauchi

A ranar Laraba, kwamitin ya bayyana cewa ƙorafin bai cika ƙa’ida ba.

Shugaban kwamitin, Sanata Neda Imasuen, ya ce Natasha ce da kanta ta sanya hannu a kan ƙorafin, maimakon wani ya sa mata hannu, wanda hakan ya sa ya zama mara inganci.

Haka kuma, ya bayyana cewa batutuwan da ke cikin ƙorafin tuni suna gaban kotu, don haka majalisa ba ta da ikon yin hukunci a kansu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Kwamitin Zaman Lafiya A Kananan Hukumomin Jahun Da Miga Na Jihar Jigawa

A wani muhimmin mataki na karfafa zaman lafiya da sulhu, gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamitocin zaman lafiya da sulhu a kananan hukumomin Jahun da Miga.

A lokacin bikin kaddamarwar, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, ya bayyana aikace-aikacen da aka dora wa kwamitocin.

Ya jaddada bukatar kwamitocin su gano musabbabin rikice-rikicen da suka addabi wasu sassan yankunan.

A cewarsa, wannan mataki yana nuna kudurin gwamnatin Gwamna Umar Namadi na tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’ummar jihar.

Ya ce an dora wa kwamitocin nauyin tantance tasirin wadannan rikice-rikice a tsakanin iyalai daban-daban, bayar da shawarwari masu inganci, tare da sanar da gwamnati duk wani muhimmin abu da ke bukatar daukar mataki.

Malam Bala Ibrahim ya ce, daya daga cikin manyan aikace-aikacen kwamitocin shi ne wayar da kan al’umma game da muhimmancin hadin kai da zama lafiya.

Ya kara da cewa, an kuma dora musu nauyin warware rikice-rikice ta hanyar sulhu tsakanin bangarorin da ke rikici.

Shugaban Kwamitin Karamar Hukumar Miga, DC Atiku Musa, ya bayyana godiyarsa bisa nadin da aka yi masa, tare da alkawarin gudanar da aikinsa bisa gaskiya da adalci don sauke nauyin da aka dora musu.

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Dr Idris Dutsen Tanshi
  • An Kaddamar Da Kwamitin Zaman Lafiya A Kananan Hukumomin Jahun Da Miga Na Jihar Jigawa
  • An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai
  • APC Ce Ke Min Bita-Da-Ƙulli Wajen Yi Min Kiranye – Sanata Natasha
  • Kotun ƙoli ta sauke Julius Abure daga shugabancin jam’iyyar LP
  • Aljeriya ta bukaci taron gaggawa a kwamitin tsaro kan Falasdinu
  • Ƙoƙarin Tsige Sanata Natasha Ya Gaza Cika Ƙa’idar Doka – INEC
  • INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye
  • Jami’ar Bayero Ta Kaddamar da shirin amfani da adaidaita Sahu wajen zirga zirga a Jami’ar
  • ICC ta yi kakkausar suka ga Hungary saboda yin watsi da sammacin kama Netanyahu