Kasar Afrika ta Kudu, ta yi Allah wadai da yadda ta ce Isra’ila ke amfani da yunwa a matsayin makamin yaki a Gaza ta hanyar toshe agajin jin kai ga Zirin tun ranar Lahadi.

Isra’ila na “amfani da yunwa a matsayin makamin yaki” a Gaza ta hanyar toshe inji Afirka ta Kudu a wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fiyar yau Laraba 5.

“Ta hanyar hana shigowar abinci a Gaza, Isra’ila na ci gaba da amfani da yunwa a matsayin makamin yaki,” in ji Pretoria, wacce dama tun tuni ta shigar da korafi kan Isra’ila akan kisan kiyashi a Gaza a gaban kotun duniya.

Afirka ta Kudu ita ce kasa ta baya-bayan nan da ta yi Allah-wadai da Isra’ila kan katse taimakon ga Gaza, wanda ta ce wata karin shaida ce ta cewa tana amfani da “yunwa” kan Falasdinawa.

A cikin sanarwa da ta fitar, “Afrika ta Kudu ta yi kakkausar suka kan kin amincewar da Isra’ila ta yi na ba da izinin shigar da agajin jin kai a zirin Gaza da kuma rufe mashigar kan iyakokinta a daidai lokacin da al’ummar Gaza ke fama da wahalhalu masu yawa da kuma bukatar abinci da matsuguni da magunguna cikin gaggawa.”

Idan ana tune a watan Janairun 2024, Afirka ta Kudu ta gabatar da karar kisan kare dangi a kan Isra’ila a gaban kotun ICJ.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: amfani da yunwa a

এছাড়াও পড়ুন:

Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya yi watsi da batun aike wa da dakarun zaman lafiya zuwa kasar Ukiraniya kamar yadda kasashen turai suke tattaunawa akai.

Ministan harkokin wajen kasar ta Rasha ya bayyana cewa, gwamnatin Amurka tana son a kawo karshen yaki, da shimfida zaman lafiya,amma kuma kasashen turai suna son a ci gaba da yaki.

Sergey Lavro ya kuma ce; tunanin aikewa da dakarun zaman lafiya zuwa Ukiraniya wauta ce.

Lavrov ya bayyana shugaban kasar Ukiraniya Zelenskiy

 da cewa dan Nazi ne, wanda ya ha’inci al’ummarsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas
  • Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace
  • Za’a yi Garambawul Kan Dokar Amfani Da Shafukan Sada Zumunta A Kasar Nijer
  • RAMADAN: Gwamnatin Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar 
  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji A Gaza
  • MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza
  • HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Noman Rani Na Zamani A Karamar Hukumar Maigatari
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya