Kasar Afrika ta Kudu, ta yi Allah wadai da yadda ta ce Isra’ila ke amfani da yunwa a matsayin makamin yaki a Gaza ta hanyar toshe agajin jin kai ga Zirin tun ranar Lahadi.

Isra’ila na “amfani da yunwa a matsayin makamin yaki” a Gaza ta hanyar toshe inji Afirka ta Kudu a wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fiyar yau Laraba 5.

“Ta hanyar hana shigowar abinci a Gaza, Isra’ila na ci gaba da amfani da yunwa a matsayin makamin yaki,” in ji Pretoria, wacce dama tun tuni ta shigar da korafi kan Isra’ila akan kisan kiyashi a Gaza a gaban kotun duniya.

Afirka ta Kudu ita ce kasa ta baya-bayan nan da ta yi Allah-wadai da Isra’ila kan katse taimakon ga Gaza, wanda ta ce wata karin shaida ce ta cewa tana amfani da “yunwa” kan Falasdinawa.

A cikin sanarwa da ta fitar, “Afrika ta Kudu ta yi kakkausar suka kan kin amincewar da Isra’ila ta yi na ba da izinin shigar da agajin jin kai a zirin Gaza da kuma rufe mashigar kan iyakokinta a daidai lokacin da al’ummar Gaza ke fama da wahalhalu masu yawa da kuma bukatar abinci da matsuguni da magunguna cikin gaggawa.”

Idan ana tune a watan Janairun 2024, Afirka ta Kudu ta gabatar da karar kisan kare dangi a kan Isra’ila a gaban kotun ICJ.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: amfani da yunwa a

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano

Janar Tukur ya yaba wa sojojin bisa jajircewa da kwarewa da suka nuna a yayin aikin, wanda ya kai ga kwato tarin makamai da alburusai da sauran su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jigawa Za Noma Rabin Shinkafa Da Ake Amfani Da Ita A Nigeria Nan Da 2030
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • ICC ta ki amincewa da bukatar Isra’ila na soke sammacin kama Netanyahu
  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano